#AdalciGaWalida (01): ƘIRA GA GWAMNATIN JIHAR JIGAWA DA TA ƊAUKI MATAKIN GAUGAWA A KAN KUƁUTAR DA WALIDA ABDULHADI
Daga Dr. Isah Billami Hadejia

__________
Muna miƙa kira na musamman ga Gwamnatin Jihar Jigawa da ta ɗauki matakin gaugawa tare da nuna cikakkiyar kulawa kan zargin da ake yi ga wani jami’in tsaro na farin kaya, IFEANYI, wnda ya sace Walida Abdulhadi da kuma sauya mata addini zuwa KIRISTANCI da cin zarafinta, ba tare da sahalewarta ko na iyayenta ba.
Wannan lamari ya shafi muhimman haƙƙoƙin ɗan Adam da Kundin Tsarin Mulki ya tabbatar da su, musamman ‘yancin kai, ‘yancin addini da kare mutunci da tsaron rayuwar ɗan ƙasa. Saboda haka, muna rokon gwamnati ta tabbatar da:
√ Gudanar da bincike mai zurfi, gaskiya da adalci ba tare da nuna son kai ba.
√ Tabbatar da lafiyar Walida Abdulhadi tare da kare martabarta.
√ Ɗaukar matakan doka da suka dace kan duk wanda aka samu da laifi, gwargwadon abin da doka ta tanada.
√ Mun yi imanin cewa ɗaukar mataki cikin gaugawa zai ƙara tabbatar da cewa gwamnati na tsayawa kan gaskiya, adalci da kare haƙƙin ‘yan ƙasa ba tare da wariya ba.
√ Kare haƙƙin ‘ya mace da mutuncin ɗan Adam ba alheri ba ne kawai, wajibi ne da doka ta shinfiɗa.
√ Yin shirun Gwamnati a kan wannan lamarin, yana nuna gazawa da nuna halayyar ko-in-kula wajen kare martabar ‘ya’yanta.
√ Sakamakon haka, muna sake ƙira da BABBAR MURYA da cewa lallai-lallai Gwamnatin Jihar Jigawa ta amsa koken al’umma a kan matsalar wannan yarinya.
__________
JAMA’A, DON ALLAH A YAƊA WANNAN SAƘO DOMIN YA ISA KUNNUWAN HUKUMOMIN DA SUKA DACE!













