RAMADAN KARIM: 02-1447

__________
Assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatuhu. ‘Yan uwa, barkanmu da ibadar azumi. Ga shi Allah ya kawo mu rana ta biyu a wannan babbar ibada, don haka bari mu yi wa juna nasiha:
Ɗaya daga cikin darussan azumi shi ne, gyaran tarbiyya, domin kuwa ana son mutum ya kasance mai kyawawan ɗabi’u a kowane lokaci na rayuwarsa, ba sai lokacin azumi kaɗai ba.
Manzon Allah, Muhammadu (saw) shi ya fi kowa kyawun halaye. Shi ne abin koyinmu, domin Allah (swt) a cikin Alkur’aninsa mai girma, Suratul Ƙalam 68:4 ya ce: “Kuma lalle kai kana kan ɗabi’a (halaye) mafi girma (mafi kyau).”
Haka kuma kamar yadda Bukhari (Hadisi mai lamba 3559) da Muslim (Hadisi mai lamba 2321) suka ruwaito, Manzon Allah (saw) yana cewa: “Mafi alherinku, shi ne wanda ya fi kyawawan halaye.”
Wannan ke ƙara tabbatar mana da cewa a wurin Allah da Manzonsa, babban al’amari shi ne kyakkyawar ɗabi’a. Babu ruwan Allah da tarin dukiyarka ko nasaba ko mulkinka. Wanda ya fi alheri a cikin mutane, shi ne mutum mafi kyawawan halaye, mai mu’amala mai kyau abar gamsarwa da amfani ga al’umma.
‘Yan uwa, mu ribaci ibadar azumi ta hanyar gyara halayenmu da ɗabi’unmu. Mu zama masu aikata alheri ga junanmu da kyautatawa. Allah sa mu dace, Amin.
__________













