• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Saturday, May 2, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Labarai

Daura Birnin Bayajidda: Janar Buratai Da Ayarinsa Sun Ziyarci Buhari Da Sarki

Sun yaba da yadda ya yi wa al'umma hidima

webmaster by webmaster
June 4, 2023
in Labarai
0
Daura Birnin Bayajidda: Janar Buratai Da Ayarinsa Sun Ziyarci Buhari Da Sarki
121
SHARES
58
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Related posts

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

April 19, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
Birgediya-Janar Sani Usman Kuka-Sheƙa (mai ritaya), shi ne Sarkin Yaƙin Kanwan Katsina, kamar kuma yadda ya kasance tsohon Kakakin Rundunar Sojojin Najeriya. Yana daga cikin na hannun daman tsohon Ambasadan Najeriya a Jamhuriyar Benin, Laftanar-Janar Tukur Yusuf Buratai (mai ritaya), OFR, Betaren Biu kuma Garkuwan Keffi. A wannan rahoto na musamman, Janar SK Usman ya bayyana yadda suka ziyarci Daura a makon nan:
A ranar Juma’ar da ta gabata (02-06-2023) na samu martabar yin rakiya ga Mai Girma Laftanar-Janar Tukur Yusuf Buratai (mai ritaya) CFR (Magayakin Ƙasar Hausa), tsohon Babban Hafsan Rundunar Sojojin Najeriya, tsohon Ambasadan Najeriya a Jamhuriyar Benin, zuwa birnin Daura mai daɗaɗɗen tarihi, a Jihar Katsina, Najeriya.
Maƙasudin ziyarar shi ne domin gaisuwa ta musamman ga babban ɗan kishin ƙasa, dattijo, tsohon Shugaban Ƙasa, Mai Girma Janar Muhammadu Buhari, GCFR kuma domin taya shi murnar kammala shugabancin Najeriya na tsawon shekaru takwas. Haka kuma mun yi masa fatan alheri da addu’ar ci gaba da samun nasara a rayuwarsa ta gaba. Haka kuma mun yi masa godiya da irin goyon baya da tagomashi da ya riƙa bai wa Janar Buratai, a lokacin shugabancin Rundunar Sojojin Najeriya. Mun yaba masa da irin yadda ya yi wa al’ummar Najeriya da ma duniya baki ɗaya hidima a tsawon shekarun mulkinsa.


Irin wannan muhimmiyar ziyara ba za ta kammala ba, ba tare da mun miƙa gaisuwa ta musamman ga Uban Ƙasa, Mai Martaba Sarkin Daura, Farouk Umar Farouk CFR ba. Don haka, wannan ziyara ta ba mu damar gabatar da Sallar Juma’a a babban masallacin Daura tare da Mai Martaba Sarki da Shugaba Buhari, sannan kuma muka ziyarci fadarsa.
Babu shakka, wannan ziyara ta ƙayatar da mu, musamman yadda ta farfaɗo mana da tarihin wannan muhimmin gari da masarauta da ta share sama da shekaru 3,000 a duniya. Wani al’amari muhimmi da ya ɗauki hankalina, shi ne irin kaifin basirar Mai Martaba Sarki da irin karsashinsa da kula da mu cikin karimci, duk kuwa da cewa ya cin ma shekara fiye da 91. Mun yi amfani da wannan dama wajen yabawa da nuna matuƙar godiyarmu da irin karimcin da ya nuna mana da ƙauna, a matsayinsa na uban al’umma.
A duk tsawon ziyarar nan tamu, an nuna mana tsantsan karimci, gami da ingantaccen abincin rana, wanda Alhaji Mamman Daura da Ambasada Muntari Ali Daura suka tanadar mana. Abokina Alhaji Rabe, sai da ya tanadar mani da sanannar “fura da nonon Daura” domin kawo tsaraba Abuja.
Babu raba ɗaya biyu, tabbas wannan ziyara za ta daɗe a zuciyata, a matsayin ɗaya daga zumunci mafi fa’ida da suka faru a rayuwata. Babu shakka na ƙaru da ilimi da zumunci da ƙauna, kamar yadda ta ƙarfafa mani gwiwar ci gaba da riƙe halayen gaskiya da amana. Lallai na ji daɗin wannan ziyara mai girma da muhimmanci, wacce ba zan iya ƙimanta ta da komai ba.
Previous Post

Rusau A Kano: Ina Bayan Gwamna Abba Gida-Gida

Next Post

Sheikh Abduljabbar Ya Kusa Samun ‘Yanci

Related Posts

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi
Labarai

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

April 19, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?
Labarai

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina
Labarai

Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina

February 13, 2026
Next Post
Sheikh Abduljabbar Ya Kusa Samun ‘Yanci

Sheikh Abduljabbar Ya Kusa Samun 'Yanci

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

RAMADAN KARIM: 25-1447

RAMADAN KARIM: 25-1447

March 14, 2026
Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (5)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (5)

February 11, 2026
Tsakanin A’isha Humaira da Umar Baana: Sulhu Alheri Ne

Tsakanin A’isha Humaira da Umar Baana: Sulhu Alheri Ne

October 31, 2025
Go Back to the Roots, Write in African Tongues – PAWA

Go Back to the Roots, Write in African Tongues – PAWA

March 18, 2024

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana
  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)
  • General Buratai (A Poem)

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

April 28, 2026
Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)

April 27, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.