TSOKACINMU NA YAU (21)
Yau Juma’a, 21-Ramadan-1446, Hijirar Manzon Allah (saw), wacce ta yi daidai da 21-Maris-2025, Miladiyya.
A tsokacinmu na yau, za mu yi nasiha ne ga juna game da HAƊAMA. Haɗama na nufin babbake komai na amfani ga mutum shi ɗaya. Misali, idan abinci ne, mutum ya ce zai ci fiye da ƙima kuma ya hana wasu.
Haɗama ta haɗa har da duk wasu abubuwan amfanin rayuwa, kamar sutura, muhalli da sauransu, duk ana samun masu yin haɗama a kansu.
Haɗama mummunar ɗabi’a ce, wacce ke cutar da mai yin ta da ma sauran al’umma da ke tare da shi. Mu kiyaye aikata ta, domin samun ribar rayuwa.
Allah sa mu dace, Amin.
Mu wuni lafiya.
Naku,
Bashir Yahuza Malumfashi,
Editan Mujallar Taskar Gizago.












