• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Friday, April 17, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Shanshani

SABON ZUMUNCI: KWANKWASO DA GANDUJE SUN YI SULHU

Shanshani by Shanshani
December 22, 2023
in Shanshani
1
SABON ZUMUNCI: KWANKWASO DA GANDUJE SUN YI SULHU

Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso da Abdullahi Umar Ganduje

23
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

SABON ZUMUNCI: KWANKWASO DA GANDUJE SUN YI SULHU

Wata majiya mai ƙarfi da ke da kusanci da tsofaffin gwamnonin Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso da Abdullahi Umar Gabduje ta shaida wa SHANSHANI cewa, jigajigan siyasar na Jihar Kano sun yi sasanci da juna.

Related posts

KAMUN LUDAYIN JEMAGE

KAMUN LUDAYIN JEMAGE (26-08-2023 da 02-09-2023)

September 2, 2023
KAMUN LUDAYIN JEMAGE

KAMUN LADUYIN JEMAGE (19-08-2023)

August 20, 2023

Al’amarin mai kama da almara ya faru ne a maraicen jiya Alhamis, inda majiyar ta ce giwayen biyu sun ɗaukar wa juna alƙawarin ɗinkewa wuri ɗaya, domin ci gaba da yi wa al’ummar Jihar Kano da ƙasa baki ɗaya hidima.

Da yake ƙarin haske dangane da wannan al’amari, wani na hannun daman Sanata Kwankwaso, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce sasanci tsakanin manyan ‘yan siyasar biyu ya tabbata ne, bayan da Ganduje ya ziyarci Kwankwaso a gidansa da ke Abuja, a jiya Alhamis.

Ya ce tsofaffin gwamnonin biyu sun killace kansu ne a ɗaki su biyu, inda suka kwashe kusan awa ɗaya suna ganawa, kafin daga bisani suka fito, inda Kwankwason ya yi wa Gabduje rakiya har ya shiga motarsa ya fita daga gidan.

“Bayan da suka fito daga ɗakin da suka gana, mun gan su suna ƙyakyata dariya, inda Kwankwaso ya raka Ganduje zuwa motarsa. A haka suka yi bankwana da juna.” A cewar na hannun damar Kwankwaso.

Alaƙa dai tsakanin Kwankwaso da Ganduje ta fara tsami ne tun daga shekarar 2015, bayan da shi Ganduje ya amshi ragamar mulkin Kano daga hannun Kwankwaso.

A haka aka yi ta tafiya cikin gaba da juna, inda ta kai ga Kwankwaso ya fita daga Jam’iyyar APC zuwa PDP, inda daga bisani kuma ya zarce zuwa Jam’iyyar NNPP.

Ko me zai biyo bayan wannan sulhu tsakanin giwayen biyu? Masu fashin baƙin alƙaluman siyasa suna ganin cewa al’amura za su inganta a siyasance a Jihar Kano, musamman zaman gaba da juna zai kawo ƙarshe, kamar kuma yadda siyasar zage-zage tsakanin magoya bayansu za ta mutu.

Haka kuma, wasu na ganin cewa wataƙila Kwankwaso da dukkan muƙarrabansa za su yi hijira daga NNPP zuwa APC.

Sai dai kuma wani al’amari da zai ɗauki hankali shi ne, yaya za ta kasance a batun shari’ar Gwamna Abba Kabir Yusuf da Yusuf Gawuna?

Ko me ke nan dai, yanzu kallo ya koma sama, inda za a saurari manyan ‘yan siyasar biyu, su bayyana wa al’umma inda suka dosa.

A cewar wani ɗan siyasa a Kano, “muddin dai Ganduje da Kwankwaso sun ɗinke wuri guda, to babu shakka su ne jagororin Jihar Kano a siyasance, yadda duk suka dama, dole haka kowa zai sha!

~~~~~~~
SANARWA:
Wannan labari, almara ce daga bakin SHANSHANI. Bai faru ba da gaske. To amma ku masu karatu, mene ne ra’ayinku? Yaya kuke gani, idan aka ce waɗannan manyan ‘yan siyasa sun sasanta da juna?
~~~~~~~

Previous Post

Minista Ga VON: Ku Yaɗa Kyawawan Labaran Nijeriya Ga Duniya

Next Post

Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnatin Tarayya Za Ta Saka Son Ƙasa A Zukatan Al’umma  – Minista

Related Posts

KAMUN LUDAYIN JEMAGE
Shanshani

KAMUN LUDAYIN JEMAGE (26-08-2023 da 02-09-2023)

September 2, 2023
KAMUN LUDAYIN JEMAGE
Shanshani

KAMUN LADUYIN JEMAGE (19-08-2023)

August 20, 2023
KAMUN LUDAYIN JEMAGE
Shanshani

KAMUN LUDAYIN JEMAGE

August 13, 2023
Next Post
Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnatin Tarayya Za Ta Saka Son Ƙasa A Zukatan Al’umma  – Minista

Yaƙi Da Ta'addanci: Gwamnatin Tarayya Za Ta Saka Son Ƙasa A Zukatan Al'umma  – Minista

Comments 1

  1. Dahiru G Shekarau says:
    1 year ago

    Congratulations,

    Reply

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

BIU: A Visit to a City on a Plateau (4)

BIU: A Visit to a City on a Plateau (4)

January 4, 2024
A Review of Boko Haram and other Security Challenges in Nigeria

A Review of Boko Haram and other Security Challenges in Nigeria

April 20, 2024
Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

January 14, 2026
One Who Sits Put would Not Know The Town

One Who Sits Put would Not Know The Town

January 4, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa
  • Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye
  • Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

April 16, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.