• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Thursday, April 16, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Siyasa

INEC Ta Nesanta Kanta Daga Zargin Baddala Ƙuri’un Zaɓen Gwamnan Kogi

Daga Wakilinmu by Daga Wakilinmu
November 15, 2023
in Siyasa
0
Zaɓen gwamna: Mutum 2,318,919 za su yi zaɓe a Imo, 1,833,160 a Kogi, 1,017,613 a Bayelsa, inji INEC

Shugaban Hukumar INEC, Farfesa Mahmud Yakubu

7
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

INEC Ta Nesanta Kanta Daga Zargin Baddala Ƙuri’un Zaɓen Gwamnan Kogi

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ce ko kaɗan ba ta baddala sakamakon zaɓen da ta aika a Manhajar Tattara Sakamakon Zaɓe (IReV) ba.

Related posts

Najeriya 2027: Yadda ADC Za Ta Murƙushe APC

Najeriya 2027: Yadda ADC Za Ta Murƙushe APC

April 9, 2026
2027: SABUWAR GUGUWAR SAUYIN SIYASA A KANO

2027: SABUWAR GUGUWAR SAUYIN SIYASA A KANO

February 24, 2026

INEC ta ce ta lura da wasu rahotanni da ta riƙa cin karo da su a kafafen yaɗa labarai, inda ake zargin ta da hargitsa sakamakon zaɓen da ta tura a manhajar IReV, na zaɓen gwamnan Jihar Kogi.

Kogi na ɗaya daga cikin jihohi uku da aka yi zaɓen gwamna, a ranar 11 ga Nuwamba. Sauran jihohin biyu su ne Imo da a Kudu maso Gabas da kuma Bayelsa a Kudu maso Kudu.

Cikin sanarwar da INEC ta fitar a ranar Talata, ta ja yankulan jama’a cewa su yi watsi da zargin hukumar ta baddala sakamakon zaɓen da ta loda a manhajar IReV.

Ta bayyana cewa wannan zargi da aka yi wa hukumar “ƙage ne kawai da ƙarairayin bugar da hankulan jama’a.”

Wannan kakkausan martani na INEC na ƙunshe cikin wata sanarwar da Kwamishinan Tarayya na hukumar, Mohammed Haruna ya fitar a ranar Talata.

Haruna ya ce: “Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta lura da wasu rahotanni da ke ɗora mata zargin baddala sakamakon yawan adadin ƙuri’un da ta loda kan Manhajar Tattara Sakamakon Zaɓe, wato IReV, a jihar Kogi. To ko ma daga ina, labarin ya fito dai ƙarya ce.

“Duk mai wata tababa ko shakku ya sani cewa sahihan adadin yawan waɗanda aka tantance karin shaidar zaɓen su na nan killace cikin Na’urar Tantance Adadin Masu Zaɓe (BVAS), wadda da ita ce ake amfani wajen tantance adadin masu rajistar da za su yi zaɓe a ranar zaɓen. Kuma adadin yawan masu zaɓen ha zai taɓa canjawa ba a cikin na’urar.”

Haruna ya ce batun duba adadin alƙaluman sakamakon zaɓe a manhaja ya danganta ne idan akwai ‘network’ ko babu.

Ya ce idan aka tura sakamakon zaɓe a IReV, to ba lallai ne ya isa a lokacin da aka tura ba. Kamar dai yadda saƙon tes na SMS ta waya ya ke, ba lallai ya isa lokacin da aka tura ba. Wani ya kan yi latti.

Daga nan sai ya ƙara da ce aikin Jami’an Zaɓe ne su danna ɗan maɓallin data kan Na’urar Tantance Masu Katin Zaɓe, wato BVAS domin tabbatar da an tura data a manhajar.

INEC ta ce babu inda ta baddala sakamakon zaɓe don a zalinci wani ɗan takara ko a fifita wani ɗan takarar kan wani.

Hukumar ta ce dukkan sakamakon zaɓen da aka gani a jihohin uku, shi ne abin da jama’a suka zaɓa, kuma shi ne INEC ɗin ta bayyana.

Haruna ya yi bayani dalla-dalla cewa babu yadda za a yi a iya baddala sakamakon zaɓen da adadin yawan rajistar da BVAS ta tantance idan an loda shi a manhajar IReV.

Idan ba a manta ba, tun a ranar zaɓe INEC ta fito ƙarara kamar yadda ta saba yi a kowane zaɓe, cewa ba ta da ɗan takarar ko ɗaya. Ɗan takara a cewar ta, na jam’iyya ne da ‘yan jam’iyya. Don haka sai wanda jama’a suka zaɓa.

Aikin INEC inji hukumar shi ne shirya zaɓe sahihi kuma karɓaɓɓe, kamar yadda a kowane lokacin ta ke yin bakin ƙoƙarin ta.

Previous Post

An Karrama Ɗanmadamin Yusufari Da Kambin Yabo Da Girmamawa

Next Post

Ƙasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Yi Tir Da Hare-Haren Sojojin Isra’ila A Zirin Gaza

Related Posts

Najeriya 2027: Yadda ADC Za Ta Murƙushe APC
Siyasa

Najeriya 2027: Yadda ADC Za Ta Murƙushe APC

April 9, 2026
2027: SABUWAR GUGUWAR SAUYIN SIYASA A KANO
Siyasa

2027: SABUWAR GUGUWAR SAUYIN SIYASA A KANO

February 24, 2026
Komawar Kwankwaso Zuwa APC: Gaba Kura Baya Sayaki
Siyasa

Abubuwan Da Za Su Iya Faruwa Idan Kwankwaso Ya Koma APC

September 28, 2025
Next Post
Ƙasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Yi Tir Da Hare-Haren Sojojin Isra’ila A Zirin Gaza

Ƙasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Yi Tir Da Hare-Haren Sojojin Isra'ila A Zirin Gaza

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

TATTAUNAWAR KHALID IMAM: Zuwa Ga Malam Bashir

TATTAUNAWAR KHALID IMAM: Zuwa Ga Malam Bashir

October 22, 2023
KAMUN LUDAYIN JEMAGE

KAMUN LUDAYIN JEMAGE

July 29, 2023
WILL ATIKU’S EXIT FROM THE PDP BRING HIM VICTORY IN 2027?

WILL ATIKU’S EXIT FROM THE PDP BRING HIM VICTORY IN 2027?

July 19, 2025
BATUN SASANCI DA ‘YAN BINDIGA A JIHAR KATSINA

BATUN SASANCI DA ‘YAN BINDIGA A JIHAR KATSINA

September 15, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa
  • Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye
  • Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

April 16, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.