MATSALAR TSARO: Saƙo Na Musamman Ga Jigajigan Arewa A Gwamnatin Tinubu
Daga Bashir Yahuza Malumfashi
~~~~~~~
Assalamu alaikum. Da fatan kuna cikin ƙoshin lafiya.
Bayan gaisuwa da girmamawa, wannan saƙo ne na musamman ga Jigajigan Arewa, waɗanda ke riƙe da ragamar TSARO a Gwamnatin Mai Girma Shugaban Ƙasa Alhaji Ahmad Bola Tinubu, wato mai girma Malam Nuhu Ribadu (Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara Ta Fuskar Tsaro) da Alhaji Badaru Abubakar (Ministan Tsaro) da Alhaji Bello Matawalle (Ƙaramin Ministan Tsaro).
A yau dai Arewa tana cikin matsalar tsaro mafi muni. A kullum sai an kashe al’umma. A kullum sai an sace mutane. A kullum sai an kassara mutane.
Rahotanni daga Jihar Sakkwato, ba su da daɗin ji ko kaɗan, domin kuwa ‘yan ta’adda sun kafa sansani, a kullum sai ɗaukar mutane suke, suna kashe wasu, suna amsar kuɗin fansa ga wasu. Ko a shekaranjiya, sun shiga Jami’ar Usman Ɗanfodiyo, sun saci kayan abinci kuma sun yi barazana ga rayukan ɗalibai.
A Jihar Zamfara kuwa, abin ya zama sai ‘lahaula walaƙuwwata…’ domin kuwa babu safiya, rana ko daren da ‘yan ta’adda ba su sacewa, kashewa da yi wa mata fyaɗe da cin zarafi. Ko a makon jiya, sai da suka shiga Jami’ar Tarayya ta Gusau, suka sace ɗalibai mata fiye da dozin ɗaya.
A Jihar Katsina ma al’amarin ya zama gagarabadau. Ƙananan hukumomin Faskari, Ɗandume, Sabuwa, Funtuwa, Malumfashi da Ƙafur da Ƙanƙara da Dutsin-ma, kullum suna fuskantar barazanar ‘yan ta’adda. A yanzu maganar da ake Allah ne kaɗai ya san adadin mutanen da ke hannun ‘yan ta’adda.
Ko a asubahin Talatar da ta gabata, ‘yan ta’adda sun shiga gidajen kwanan ɗaliban Jami’ar Tarayya ta Dutsin-ma, suka sace ɗalibai mata guda biyar.
A sanadiyyar rashin tsaro a Arewa, tattalin arziƙinmu na noma da kiwo da kasuwanci duk sun ɓalɓalce. An kassara harkar ilimi, domin kuwa ɗalibanmu maza da mata suna cikin barazana. Al’amura sun durƙushe.
Ya masu girma shugabannin tsaro, don Allah ku yi abin da ya dace, ku haɗa kan Gwamnonin Arewa da Sarakuna da Malaman Addinai da Manyan Attajirai da dukkan shugabannin Arewa domin tattauna hanyar kawo ƙarshen wannan babbar matsala. Shin haka za ku zuba ido ANA TA KASHE MU?
~
A’A – wajibi ne ku yi abin da ya dace, domin kawo mana ƙarshen wannan fitina. Ku ne idanunmu da kunnuwanmu a wannan gwamnati ta Shugaba TINUBU. Allah Ya ba ku ikon yin abin da ya dace. Amin-summa-Amin!
~~~~~~~
Daga Bashir Yahuza Malumfashi,
Babban Editan Mujallar Taskar Gizago
~~~~~~~












