Gwamna Ya Rantsar da Sabbin Manyan Sakatarori A Jihar Katsina
Daga Bashir Yahuza Malumfashi
__________
Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya rantsar da sabbin Manyan Sakatarori guda huɗu, inda ya jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta yi sassauci wajen tabbatar da cancanta, gaskiya da adalci a harkokin gudanar da mulki ba.
Sabbin Sakatarorin da aka rantsar sun haɗa da Malam Abdu Usman, Dakta Sani Suleiman, Dakta Shamsuddeen Yahaya Suleiman da Dakta Hussaini Hamisu Yanduna. An gudanar da bikin rantsarwar ne a ranar Laraba, 5 ga Agustan 2026, a Gidan Gwamnatin Jihar Katsina.

Da yake jawabi bayan rantsar da su, Gwamna Raɗɗa ya bayyana cewa an zaɓi sabbin jami’an ne bisa cancanta, ƙwarewa da jajircewa wajen aiki, ba tare da la’akari da alaƙa, sanayya ko wani tasiri na daban ba.
Ya buƙaci sabbin Sakatarorin da su gudanar da ayyukansu cikin gaskiya, riƙon amana da adalci, yana mai bayyana cewa irin waɗannan kyawawan ɗabi’u ne za su taimaka wajen ƙara inganta ayyukan gwamnati da kuma samar da ingantacciyar hidima ga al’ummar Jihar Katsina.
Gwamnan ya kuma tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da aiwatar da tsarin da ke tabbatar da adalci wajen ba da damar ci gaban ma’aikatan gwamnati, domin ƙarfafa ƙwazo da haɓaka ingancin aikin gwamnati.
Hakazalika, ya yi kira ga manyan jami’an gwamnati da su mayar da hankali wajen horar da matasa ma’aikata tare da koya masu aiki, su goge, domin samar da ƙwararrun ma’aikatan da za su ci gaba da tafiyar da harkokin gwamnati cikin inganci a nan gaba.
Bikin rantsarwar ya nuna wani mataki na ci gaba a ƙoƙarin gwamnatin Malam Dikko Umaru Radda na ƙarfafa tsarin aikin gwamnati ta hanyar bai wa ƙwararru damar jagorantar manyan sassan gudanarwa, domin inganta ayyukan gwamnati da bunƙasa hidimomin da ake kai wa al’ummar jihar.
__________













