Saƙon Godiya Da Bangajiya
__________
Al’ummar Ƙaramar Hukumar Malumfashi, muna ƙara miƙa saƙon godiya da bangajiya zuwa ga Mai Girma, Gwamnan Jihar Katsina, Dakta Dikko Umar Radda, PhD, bisa wannan ziyara ta buɗe ayyukan hanyoyi da Mai Girma Gwamna ya ƙaddamar, a cikin Ƙaramar Hukumar Malumfashi.

Muna godiya sosai. Allah ya ƙara daga darajar Karamar Hukumar Malumfashi. Allah ya ƙara kawo mana zaman lafiya da cigaba a garinmu da ƙasa baki ɗaya.
__________
Saƙo Daga Mukhtar Abdullahi City,
Shugaban Ƙaramar Hukumar Malumfashi
(22-07-2026)
__________











