• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Saturday, June 13, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Babban Labari

GURƁATACCEN HATSI: An Ja Hankalin Hukumomin Jihar Katsina

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
August 20, 2023
in Babban Labari
0
GURƁATACCEN HATSI: An Ja Hankalin Hukumomin Jihar Katsina

Wata gurɓatattar masara da ake zargin raba wa mutane

76
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

GURƁATACCEN HATSI: An Ja Hankalin Hukumomin Jihar Katsina

 Hankalin al’umma a Jihar Katsina ya tashi, yadda aka samu bayyanar wani gurbataccen hatsi, musamman masara da shinkafa a hannun mutane.

Related posts

Sojan Gona: An Kama Sojan Bogi Mai Muƙamin Manjo-Janar

Sojan Gona: An Kama Sojan Bogi Mai Muƙamin Manjo-Janar

June 12, 2026
Kotu Ta Ayyana Hausawa Da Fulani Halastattun ‘Yan Ƙasa A Jihar Filato

Kotu Ta Ayyana Hausawa Da Fulani Halastattun ‘Yan Ƙasa A Jihar Filato

June 11, 2026

An yi zargin cewa, hatsin na daga cikin

Gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa

wanda Gwamnatin Jihar Katsina ke rabawa ne ga mabuƙata a matsayin tallafin rage raɗaɗin matsin rayuwa da ake ciki. Da yake tsokaci game da al’amarin, mai sharhi kan al’amuran yau da kullum kuma mai tallafa wa marasa galihu a Jihar Katsina, Malam Muhammad Aminu Kabir ya zargi wasu daga cikin ‘yan kwangilar da gwamnati ta ba aikin samar da hatsin, inda ya roƙe su da su ji tsoron Allah, su gyara lamarinsu.

“Don Allah ‘yan Kasuwa ko ‘yan kwangilar da aka ba damar kawo wa al’ummar Jihar Katsina tallafin masara, ku ji tsoron Allah…” in ji Muhammad.

Ya ci gaba da cewa, “bayanai daga mabambantan wurare na nuni da cewa masarar da ake rabawa, an yi amaja a cikin ta. Ma’ana, an gauraya sabuwa da tsohuwa a wuri guda, sannan wata ma ta fara lalacewa.”

Ya ce akwai buƙatar waɗanda aka ɗora wa wannan alhakin, su kula da duk wanda suka bai wa damar kawo masarar nan. “Idan ya kawo marar kyau, ya ƙwashe abinsa, kar su yadda a ba da abin da zai iya cutar da al’umma,” kamar yadda Muhammad Aminu ya bayyana.

A Malumfashi Jihar Katsina kuwa, wasu mutane sun koka ne game da gurɓatattar shinkafar da ake rabawa, a matsayin tallafin rage matsin rayuwar da ake ciki. Kamar yadda wani mazaunin garin, Malam Aliyu Umar S/Gini ya koka game da gurɓatattar shinkafar, ya ce: “Yanzu wani ya zo shagona, ya gaya mani cewa shinkafar da Gwamna Dikko Raɗɗa ya raba, wari take, sai ƙudaje ke bin ta.”

Wakilinmu ya tuntuɓi Babban Mataimaki Ga Gwamnan Jihar Katsina Kan Al’amuran Watsa Labarai, Malam Maiwada Ɗammallam, ta wayar tarho, domin jin bahasin gwamnati kan lamarin. Ya bayyana cewa babu shakka ya samu rahoton da wasu kafafen watsa labarai suka wallafa kan lamarin. Sai dai ya ce ba su bayyana hakikanin wuraren da aka samu gurɓataccen hatsin ba.

“Tabbas akwai tallafin hatsi kala biyu da gwamnati za ta raba, ɗaya daga Gwamnatin Tarayya, ɗaya kuma daga Gwamnatin Jiha. Ya zuwa yanzu hatsin tallafi daga Gwamnatin Tarayya bai zo ba, balle a fara rabawa. Shi kuma na Jihar Katsina, an ɗora aikin sanarwar da rabawa ga dukkan ƙananan hukumomin jihar, su za su sayi hatsin kuma su raba shi, ” in ji Malam Maiwada.

Ya ƙara da cewa, kasancewar kowace ƙaramar hukuma ce ke da alhakin raba hatsin, akwai yiwuwar a samu wani ɓangare da matsala, kasancewar ‘yan kwangila ne da yawa kuma daban-daban.

“Ya zuwa yanzu dai, a hukumance, har yanzu ba mu samu sahihin ƙorafi kan haka ba. Yana da kyau kafafen watsa labarai su zurfafa bincike, domin tabbatar da hakikanin wuraren da aka samu irin wannan matsalar, domin a gyara.” A cewar Malam Maiwada Ɗammallam.

Gurɓatattar masara da ake zargin ana rabawa a Jihar Katsina

Ya zuwa yanzu dai, al’umma na kokawa kan lamarin, inda suka nemi Gwamnatin Jihar Katsina ta binciki al’amarin kuma ta magance matsalar, domin gudun kada hatsin ya haddasa cuta ga al’umma.

Previous Post

KWATAM HUBA HALIMA TAHIR: Tattaunawa Da Fitattar ‘Yar Jarida Basarakiya

Next Post

KAMUN LADUYIN JEMAGE (19-08-2023)

Related Posts

Sojan Gona: An Kama Sojan Bogi Mai Muƙamin Manjo-Janar
Babban Labari

Sojan Gona: An Kama Sojan Bogi Mai Muƙamin Manjo-Janar

June 12, 2026
Kotu Ta Ayyana Hausawa Da Fulani Halastattun ‘Yan Ƙasa A Jihar Filato
Babban Labari

Kotu Ta Ayyana Hausawa Da Fulani Halastattun ‘Yan Ƙasa A Jihar Filato

June 11, 2026
Ta Banka Wa Mijinta, Kishiyarta Da Yara Wuta A Kano
Babban Labari

Ta Banka Wa Mijinta, Kishiyarta Da Yara Wuta A Kano

May 13, 2026
Next Post
KAMUN LUDAYIN JEMAGE

KAMUN LADUYIN JEMAGE (19-08-2023)

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

UEFA 2025: WACE ƘUNGIYA CE ZA TA ƊAUKI KOFIN ZAKARU?

UEFA 2025: WACE ƘUNGIYA CE ZA TA ƊAUKI KOFIN ZAKARU?

April 28, 2025
Zaɓen gwamna: Mutum 2,318,919 za su yi zaɓe a Imo, 1,833,160 a Kogi, 1,017,613 a Bayelsa, inji INEC

INEC Ta Yi Wa Daraktocin Hukumar Huɗu Ritayar Dole

December 28, 2023
RAMADAN KARIM: 19-1447

RAMADAN KARIM: 19-1447

March 8, 2026
Nigerian Politicians: Leaders or Looters?

Nigerian Politicians: Leaders or Looters?

June 8, 2024

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Inna Lillahi… We Lost Gen. Rabe
  • FIFA World Cup 2026: Yau Akwai Gumurzu Tsakanin Brazil Da Morocco
  • Yau Za A Fafata Tsakanin Canada Da Bosnia-Herzegovina

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Inna Lillahi… We Lost Gen. Rabe

Inna Lillahi… We Lost Gen. Rabe

June 13, 2026
FIFA World Cup 2026: Yau Akwai Gumurzu Tsakanin Brazil Da Morocco

FIFA World Cup 2026: Yau Akwai Gumurzu Tsakanin Brazil Da Morocco

June 13, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.