RAMADAN KARIM: 14-1447

__________
‘Yan uwa, ina yi maku sallama irin ta Musulunci, Assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatuhu. Bayan haka, a yau Talata, Allah ya nuna mana rana ta 14 a Ramadan. Yau ma ga ‘yar nasiha:
A yau nasiharmu tana kira ne zuwa ga juriya tare da haƙuri a rayuwa. Haka kuma tana nuna muhimmancin taimako. Lallai babu wani abu na tsanani da ke ɗorawa.
Allah mai girma da ɗaukaka yana cewa a cikin Suratul Inshirah 94:5-6: “Tare da wahala akwai sauƙi.” Haka kuma a Hadisin Muslim mai lamba 2699, daga Abu Huraira (RA) ya ce Manzon Allah (saw) ya ce: “Duk wanda ya sauƙaƙa wa mumini wata damuwa daga damuwoyin duniya, Allah zai sauƙaƙa masa wata damuwa daga damuwoyin ranar ƙiyama.”
Ya Allah, ka sa mu cikin masu juriya a lokacin tsanani. Ka sa mu cikin masu taimako duk lokacin da muke da iko kuma ka sanya mu cikin masu godiya ga ni’imominka. Amin-Summa-Amin.
__________












