RAMADAN KARIM: 11-1447

__________
‘Yan uwa, ina yi maku sallama irin ta Musulunci, Assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatuhu. Bayan haka, a yau Asabar, Allah ya nuna mana rana ta 11 a Ramadan. Yau ma ga ‘yar nasiha:
‘Yan uwa, a yau nasiharmu tana ishara ne zuwa ga muhimmancin da ke tattare da godiya. A duk lokacin da wani ya amfanar da kai, to ka nuna godiyarka a gare shi ko gare ta. Wannan zai ƙara jin daɗi da fahimta a tsakaninku.
Yin godiya wani babban sinadari ne na ƙara samun albarka tare da kyautata zamantakewa. Mu zama masu gode wa Allah a kan ni’imar da ya yi mana, sai ya ƙara mana.
Allah (swt) a Alkur’ani mai girma, Suratu Ibrahim 14:7 ya ce: “Idan kuka gode, zan ƙara muku.” Manzon Allah (saw) a Hadisi ruwayar Abu Dawud (lamba 4811) da Tirmizi (lamba 1954) ya ce: “Wanda bai gode wa mutane ba, bai gode wa Allah ba.”
Muna roƙon Allah ya sanya mu cikin masu godiya ba masu butulci ba. Ya Allah mun gode da ni’imominka, Allah ka ƙara mana! Amin-Summa-Amin!
__________













