• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Friday, July 10, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Labarai

Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
February 13, 2026
in Labarai
0
Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina

Sheikh Mutawakkil Mustapha yana hausawa da Gwamna Dikko Raɗɗa

40
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Rundunar Sojojin Najeriya Ta Karrama Tsofaffin Dakarunta

Rundunar Sojojin Najeriya Ta Karrama Tsofaffin Dakarunta

July 7, 2026
Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

April 19, 2026
Sheikh Mutawakkil Mustapha yana hausawa da Gwamna Dikko Raɗɗa

 

__________

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya rantsar da Sheikh Mutawakkil Mustapha Salis a matsayin Mai Girma Alƙalin Shari’a (Khadi) na Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Shari’a ta Jihar Katsina, tare da jan hankalinsa da ya riƙa aiki da gaskiya, adalci, da tsoron Allah wajen gudanar da aikinsa.

Bikin rantsuwar, wanda aka gudanar a jiya Asabar a Gidan Gwamnatin Jihar Katsina, ya samu halartar manyan baƙi daga ɓangarorin zartarwa, majalisa da shari’a na gwamnatin ta jiha, sarakunan gargajiya, malaman addinin Musulunci da ‘yan uwa da abokan arziki.

A wata takardar manema labarai, wacce Ibrahim Kaula Mohammed, Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamnan Jihar Katsina ya sanya wa hannu, ya bayyana cewa Gwamna Radda ya bayyana naɗin a matsayin wani mataki na ƙarfafa tsarin shari’ar Musulunci da inganta isar da adalci a faɗin jihar.

“Yau muna rantsar da sabon Mai Girma Alƙalin Shari’a na Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Shari’a ta Jihar Katsina. Wannan naɗi yana ƙarfafa tsarin shari’armu tare da inganta isar da adalci ga al’ummarmu,” in ji Gwamnan.

Ya taya sabon Alƙalin murna tare da yaba wa Hukumar Ayyukan Shari’a ta Jiha, kan gudanar da cikakken tsari na zaɓe bisa cancanta.

“Ofishinka babban nauyi ne. Dole ne ka riƙa tuna rantsuwar da ka yi kuma ta zama jagora ga ayyukanka. Dole ne a yi adalci ba tare da tsoro ko son rai ba,” in ji shi.

Gwamna Radda ya tunatar da sabon Alƙalin cewa mukaminsa amana ce mai girma a gaban Allah da al’umma. Yana mai kira gare shi da ya kasance mai bin adalci, gaskiya da koyarwar Musulunci.

“Bangaren shari’a shi ne mafaka ta ƙarshe ga talaka. Amincewar jama’a tana dogara ne kan gaskiya da ƙwazon ma’aikatan shari’a,” a cewar Gwamna.

Gwamnan ya kuma sake jaddada aniyar gwamnatinsa ta ci gaba da tallafa wa ɓangaren shari’a tare da inganta haɗin gwiwa tsakanin ɓangarori uku na gwamnati, domin tabbatar da zaman lafiya, tsari da adalci a jihar.

Daga cikin waɗanda suka halarta akwai Sakataren Gwamnatin Jiha, Abdullahi Garba Faskari; Kwamishinar Shari’a kuma Babbar Lauyan Jiha, Barrista Fadila Muhammad Dikko; da Babban Alƙalin Shari’a na Jihar Katsina, tare da sauran manyan baƙi.

Previous Post

Musulmin Kudancin Najeriya Sun Jaddada Mubaya’a Ga Sarkin Musulmi

Next Post

TSAKANIN ALI JITA DA SOJABOY: WANE NE YA FI GASKIYA?

Related Posts

Rundunar Sojojin Najeriya Ta Karrama Tsofaffin Dakarunta
Labarai

Rundunar Sojojin Najeriya Ta Karrama Tsofaffin Dakarunta

July 7, 2026
Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi
Labarai

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

April 19, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?
Labarai

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
Next Post
TSAKANIN ALI JITA DA SOJABOY: WANE NE YA FI GASKIYA?

TSAKANIN ALI JITA DA SOJABOY: WANE NE YA FI GASKIYA?

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

A Review of “Leadership in the Nigerian Civil Service…”

A Review of “Leadership in the Nigerian Civil Service…”

July 8, 2025
BUKAR USMAN: The Human Library

BUKAR USMAN: The Human Library

May 19, 2026
Sasanci Da ‘Yan Bindiga: A Sake Duba Lamarin Nan A Tsanaki

Sasanci Da ‘Yan Bindiga: A Sake Duba Lamarin Nan A Tsanaki

October 13, 2025
Let’s Speak Our Mother Tongue

Mu Yi Kishi Da Alfahari Da Harshen Uwa

March 6, 2026

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Tarihin Waƙar Yaƙin Tabuka

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Afirka Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya Na Bana
  • Book Launch Seeks to Rewrite Lassa’s Story, Preserve Cultural Heritage
  • Zaɓen 2027: Akwai Yiwuwar Farfesa Pantami Ya Yi Nasara – Farfesa Lawanti

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Afirka Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya Na Bana

Afirka Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya Na Bana

July 10, 2026
Book Launch Seeks to Rewrite Lassa’s Story, Preserve Cultural Heritage

Book Launch Seeks to Rewrite Lassa’s Story, Preserve Cultural Heritage

July 9, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.