Ƙungiyar Matan Al’ummar Bura Sun Karrama Dr. Bukar Usman Bisa Cika Shekaru 83
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

__________
Ƙungiyar Bunkasa Rayuwar Matan Al’ummar Bura (Bura Women Development Association – BUWDA), ta ziyarci shahararren marubuci kuma ƙwararren masanin tsaro, Dokta Bukar Usman, OON domin taya shi murna da farin cikin zagayowar ranar haihuwarsa.
Marubucin, wanda a ranar 10-12-2025 ya cika shekaru 83 a duniya, ya amshi baƙuncin shugabannin ƙungiyar matan ta BUWDA a gidansa da ke Unguwar Maitama, Abuja, waɗanda suka miƙa masa kyautar kanbin-zayyana (roll-up banner) mai ƙayatarwa a matsayin abin tunawa da taya murna.
A rahoton Hukumar Dillancin Labarai ta Najeriya (NAN), Bukar Usman wanda aka haifa a shekarar 1942 a Biu, Jihar Borno, tsohon Babban Sakataren ne a Fadar Shugaban Ƙasa kuma shi ne Shugaban Ƙungiyar Adabin Gargajiya ta Najeriya (Nigerian Folklore Society – NFS), sannan kuma Shugaban Gidauniyar Dr. Bukar Usman.
Uwargida Ladu Gali, Muƙaddashiyar Shugabar Ƙungiyar BUWDA, yayin miƙa kyautar a Abuja, ta yaba wa Usman bisa jajircewarsa wajen tallafa wa rayuwar mabuƙata da masu rauni a cikin al’umma da kuma gudunmawar da yake bayarwa wajen karewa da bunƙasa al’adu masu tarin daraja na ƙasar Bura.
Rubutun da ke jikin zayyanar, shi ne: “Ya ranka ya daɗe, Dr. Bukar Usman, Ubanmu, Kawunmu kuma Jagoranmu, mutum mai dattaku da gaskiya. Muna taya ka murnar wannan babbar rana ta zagayowar haihuwarka.
“Kai wata kyauta ce daga Allah ga ƙasar Bura. Mutum mai tsoron Allah kuma mai halaye abin koyi. Shugaba nagari, jajirtacce kuma abin dogaro, mai kulawa da tausayi.
“Yayin da kake bikin wannan rana ta musamman, muna roƙon Allah ya yi maka dukkan nau’o’in albarka, fiye da abin da zuciyarka ta taɓa muradi.
“Allah Maɗaukakin Sarki ya ƙara maka lafiya da kwanciyar hankali. Ya kuma cika maka burin zuciyarka, yayin da kake tsufa cikin yalwar rahamarsa. Amin.”
A nasa ɓangaren, yayin da yake tattaunawa da Hukumar Dillancin Labarai ta Najeriya (NAN), Usman ya nuna godiyarsa ga wakilan Ƙungiyar BUWDA, bisa kyakkyawar ƙauna da sadaukarwar da suka nuna wajen taya shi murna.
Usman ya gode wa Allah Maɗaukakin Sarki bisa tsawaita masa rayuwa zuwa wannan lokaci da kuma albarkar da Allah ya yi masa da iyalansa gaba ɗaya. Ya shawarci abokan zamaninsa da su kasance masu godiya ga Allah bisa ni’imar tsawaita rayuwarsu, duk da ƙalubalen da duniya ke fuskanta a yau.
Ya jaddada cewa suna buƙatar ƙarin albarka daga Allah a ranaku, watanni da shekarun da Allah Ya ƙaddara musu nan gaba. Ya yi addu’ar Allah ya zuba albarka mai yawa a kan matasa. A cewarsa, duniya na ƙara zama kamar ƙauye guda ɗaya kuma tasirin da ke fitowa daga muhalli na kusa da na nesa, mai kyau da mara kyau, na iya zama mai ƙarfi ƙwarai.
Ya ce: “Babban nauyin gwamnati ne ta magance wasu matsalolin da ke shafar tsaro da jin daɗin al’umma. Ina kira ga gwamnati da ta ba da fifiko ga walwalar jama’a da tsaron rayukansu, tare da tabbatar da samar da cigaba na bai ɗaya ga kowa da kowa a ƙasar nan.”
Ambasada Abdullahi Shehu, a nasa saƙon girmamawa ga Dr. Usman, ya bayyana ranar a matsayin wani muhimmin mataki a cikin fiye da shekaru 80 na rayuwarsa. Ya ce: “Cikar shekaru 83 abin ban sha’awa ne, domin abu ne mai wuya mutum ya kai waɗannan shekaru har 83 cikin armashi kuma abin koyi.
“Ina taya ka, iyalanka da masoyanka wajen gode wa Allah Maɗaukakin Sarki bisa rahamarsa a kanka da iyalanka. A matsayinka na shugaba a hidimar jama’a, ka bar gagarumin tarihi a fagen aikin gwamnati da kula da tsaro musamman a Najeriya kuma sunanka ya riga ya shiga cikin shafukan tarihin ƙasa.
“A matsayinka na jagoranmu, ba za mu taɓa gajiya da gode maka bisa tarbiyya da koyarwar da kake ba mu ba. Allah ya ci gaba da yi maka albarka da tsawon rai cikin ƙoshin lafiya da lafiyayyen hankali.”
NAN ta ruwaito cewa daga cikin waɗanda suka taya shi murna, akwai ’yan uwansa na jini a gida da ƙasashen waje, abokai da masu yi masa fatan alheri, ciki har da ƙungiyoyi da kamfanoni daban-daban.
__________













