Ɗaliban Kebbi Sun Shaƙi Iskar ‘Yanci
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

__________
Ɗaliban nan da aka sace a makon jiya, na makarantar Government Girls Comprehensive Senior Secondary School (GGCSS) Maga, a Ƙaramar Hukumar Danko/Wasagu ta Jihar Kebbi, sun samu ‘yancinsu a yau Talata, ta hanyar amfani da tattaunawa da tsakanin jami’an Gwamnatin Tarayya da kuma ɓarayin da suka sace su.
Kafar watsa labarai ta PRNigeria ta ruwaito cewa sakin dukkan ɗaliban da aka yi garkuwa da su, ya samu ne ta hanyar haɗin gwiwa tsakanin jami’an Ofishin Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (ONSA) da kuma Hukumar Tsaro ta DSS, waɗanda suka jagoranci sasanci da mutanen da suka yi garkuwa da su.
Amfani da dabarar sulhu, wadda galibi ta ƙunshi tattaunawa da yarjejeniya, maimakon amfani da ƙarfin soja, tana nuna sabon salo da gwamnati ke bi wajen magance matsalar garkuwa da mutane da ta addabi Arewacin Najeriya.
Sace ɗaliban, wanda ya biyo bayan makamantan lamarin da suka faru a wannan yanki, ya haifar da damuwa mai yawa a faɗin ƙasa, inda har sai da Babban Hafsan Soja ya ba da umarni na musamman ga dakarun ƙasa, da su ƙara ƙaimi wajen bincike da ceto. Sakin ɗaliban ya kasance babban abin farin ciki ga iyalansu da al’umma baki ɗaya.
_______________











