Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Ɗan Majalisa Aminu Acid
~~~~~~~
Daga Abduljalal Ɗayyabu
~~~~~~~
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Maɗaukakin Sarki, mai kowa, mai komai, wanda ya ƙagi shugabanci da kuma shugaba.
Wannan buɗaɗɗiyar wasiƙa ce zuwa ga Ɗan Majalasar Dokoki ta Jihar Katsina, mai wakiltar Ƙaramar Hukamar Malumfashi, Aminu Ibrahim Sa’id Acid.
Al’ummar Mazaɓar Na’alma suna ƙara tunatar da kai alƙawuran da ka ɗaukar masu a lokacin yaƙin neman zaɓenka na farko da na biyu. Musamman hanyar da ta tashi daga Babban Duhu da ke cikin Mazaɓar Dayi zuwa Karo, Garangozai, Gidan Mai Jumina da ke Mazaɓar Na’alma, har zuwa Ɗandashire da ke Ƙaramar Hukumar Ƙanƙara.
Al’ummar wannan karkara suna cikin mawuyacin hali, musamman wajen kai mutane asibiti a lokacin damina. Mutum yana ji yana gani naƙuda za ta kama matarsa, ko yaronsa bai lafiya, ko shi karan kansa, wannan mai naƙuda ko mara lafiya zai mutu amma a kasa kai shi asibiti saboda rashin hanya.
Abu na biyu da nake son sanar da kai shi ne, wannan yanki na manoma ne amma saboda sashin hanya, mutum yana ji yana gani dole ya ƙyale abin da ya noma ko wata dukiya tasa.
Idan har Allah Ya sa suka samu wannan hanya, to za su samu sauƙi sosai, nusamman wajen taƙaita salwantar rayukan mutane da dukiyoyinsu.
Na uku, wannan yanki na Mazaɓar Na’alma, yana ɗaya daga cikin yankunan da suka fi matsala ta fuskar tsaro da ake fama da ita a Ƙaramar Hukumar Malumfashi. Kullum jama’ar wannan mazaɓa suna barin garuruwansu ne sakamakon rashin zama lafiya a wannan yanki.
Idan har wannan hanya ta samu to za a samu sauƙi ƙwarai matuƙa wajen taimaka wa jama’an tsaro, domin su shigo wannan yanki, domin su kawo wa al’ummar wajen taimakon gaugawa.
Akwai jami’an tsaro sosai a wannan ƙaramar hukuma ta Malumfashi, domin kuwa akwai Area Commander na shiyya, akwai kuma barikin sojoji amma rashin hanya zuwa karkarar Wannan ce ya sanya ko da an kiraKaramar Hukamar waɗannan jami’an tsaron, ba su zuwa kawo tallafinsu ga wannan wajen. Suna duba cewa kafin ma su zo, ‘yan ta’addar sun wuce ko kuma saboda rashin sanin hanya ga jami’an tsaron.
Don haka al’ummar wannan yanki suke neman taimakon ujila daga Ɗan Majalasar wannan yankin asu ko kuma masu faɗa a ji n wannan yanki, da ma ‘yan soshiyalmidiya, domin isar da saƙo ga Gwamnatin Jihar Katsina dangane da wannan matsala ta hanya.
Al’ummar wannan yanki suna fatan Ɗan Majalasa Aminu Ibrahim Sa’id Acid da ya duba girman Allah, ya isar masu sa saƙonsu zuwa inda za a share masu kukansu.
Daga ƙarshe muna roƙon Allah Ya kawo zaman lafiya a wannan yanki da Jihar Katsina da ma ƙasa baki ɗaya.
~~~~~~~
Saƙo daga Abduljalal Ɗayyabu, Ƙaramar Hukumar Malumfashi, Jihar Katsina.
~~~~~~~













