Ba Mu Da Wata Ƙasa Kamar Najeriya
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

•••••••
Najeriya ita ce ƙasa ɗaya tilo, abin tinƙahonmu. A duniya gaba ɗaya, ƙasa ita ce ginshiƙin martaba da mutuncin al’umma. Ba mu da wata ƙasa kamar Najeriya, domin ita ce tushen asalinmu, harshenmu, al’adunmu da tarihinmu.
Duk wani ɗan Najeriya, ko yana cikin gida ko ƙetare, haƙiƙanin gaskiya shi ne babu wani wuri da zai maye gurbin ƙasar da ta haife shi. Don haka, kishin ƙasa ba kawai jin magana ba ne, wajibi ne ga kowane ɗan ƙasa ya daraja, ya mutunta, ya kuma kare martabar Najeriya.
Kishin ƙasa yana da matuƙar muhimmanci da tasiri ga jama’ar ƙasa. Kishin ƙasa shi ne soyayya, girmamawa da jajircewar kare martabar ƙasa a kowane hali. Idan babu kishin ƙasa, to za a rasa zaman lafiya, haɗin kai da ci gaba. Idan muka kula da muhalli, muka guji cin hanci da rashawa, muka mutunta juna, to muna nuna kishin Najeriya ne. Hakan yana taimakawa, domin duniya ta girmama mu, ta ɗauke mu a matsayin al’umma mai daraja. Kishin ƙasa ba na gwamnati kaɗai ba ne, kowa yana da rawar da zai taka. Matasa, dattawa, maza da mata, dole ne mu tallabi ƙasarmu a kowane hali.
Najeriya ƙasarmu, ƙasa ce mai albarka. Tana da albarkatun man fetur, noma, ma’adinai, matasa, da al’adu masu ƙayatarwa. Akwai ƙasar noma a Arewa, igiyoyin ruwa da kasuwanci a Kudu, fasaha a Gabas da ƙarfin masana’antu a Yamma. Duk da matsalolin da muke fuskanta na rashin tsaro, talauci da siyasa mara adalci, bai kamata hakan ya sa mu watsar da ƙasarmu ba. Duniya ta san mu da ƙarfinmu, yawanmu da hikimarmu. Idan ba mu tsare ta ba, wa zai tsare mana ita?
Ya zama wajibi mu kare ƙasarmu, mu ba ta goyon bayan kuma mu taimaki juna. Yana daga cikin kishin ƙasa mu kare mutuncin Najeriya daga ɓata suna, rabuwar kai da ƙiyayya a tsakanin ƙabilu ko addinai. Ya kamata mu tallafa wa junanmu, mu zaɓi shugabanni nagari, mu yi adalci da gaskiya. Komai ra’ayi ko bambancin ƙabila, mu tuna da cewa duka jininmu ɗaya ne, ‘yan Najeriya. In mun zage damtse, mun yi aiki tare, to Najeriya za ta zama abin koyi ga sauran ƙasashe.
Lallai ne mu tashi tsaye don mu taimaki ƙasarmu. Mu sani fa cewa muna da ƙasa guda ce tal, Najeriya. Ba za mu sami wata Najeriya ta biyu ba idan muka lalata wannan. Saboda haka, mu kasance masu ƙaunar ƙasa ta hanyar aikata alheri, adalci da mutunta doka. Mu koya wa yara soyayya da alfahari da alamar tutar ƙasa. Idan kowa ya ce “Najeriya ce gidana, kuma zan kyautata ta,” to tabbas za mu ga canji mai amfani. Najeriya tamu ce kuma ba mu da wata ƙasa kamar ta.
_______________













