Ta’aziyyar Malam Nata’ala Mai Sittin Goma
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

_______________
Babu shakka, kowane mai rai mamaci ne kuma ajali ba ya taɓa wuce ranarsa. Bisa ga wannan ƙauli, a jiya Lahadi, 11-05-1447 (Hijiriyya), 02-11-2025 (Miladiyya), na samu rahoton cewa Allah ya amshi ran bawansa, Mato Yakubu, wanda aka fi sani da Malam Nata’ala Mai Sittin Goma.
Wane ne Malam Nata’ala? Kamar yadda aka bayyana a gabatarwa, sunansa Mato Yakubu kuma an haife shi a ranar 15 Agusta 1967 a garin Dambuwa Rijiya, Ƙaramar Hukumar Potiskum, Jihar Yobe.
Ya fara harkar fim ko kuma wasan kwaikwayo da daɗewa, tun ma kafin bayyanar finafinan Kannywood. Ya yi wasan kwaikwayo a garin Jimeta da ke Jihar Adamawa. Daga bisani ne ya koma Kano da sana’arsa ta fim.
Kasancewar ya fi ƙwarewa a finafinan barkwanci, a can shekarun baya, ya yi finafinai masu tarin yawa tare da marigayi Labiru Musa, wanda aka fi sani da Ɗan Ibro. Kodayake ya fi shahara a fim mai dogon zango na Daɗin Kowa, wanda gidan talabijin na Arewa24 yake haskawa. Hasali ma, a cikin wannan fim ne ya samu wannan suna na Malam Nata’ala.
Baya ga Daɗin Kowa, Malam Nata’ala ya taka rawa mai burgewa a fim ɗin A Duniya, inda nan ma ya fito a matsayin malamin tsangaya, mai almajirai.
Malam Nata’ala ya ɗan jima yana jinya, amma a watan Agustan bana ne rahoton rashin lafiyarsa ya bayyana sosai, inda ya yi fama da ciwon daji. A wani faifan bidiyo, an nuno marigayin yana maganar cewa: “Ina buƙatar taimakon addu’a da kuɗi saboda jinya ce mai hatsari kuma ƙarfina ya gaza, duk sati uku zan yi allurar Naira 250,000 har na wata shida, ban da magunguna da kuɗin gado.”
Ya samu tausayawa daga mutane daga sassa daban-daban na Najeriya. Ya kuma samu tallafi daga fitattun abokan sana’arsa ‘yan fim amma babban tallafin kuɗin da ya samu daga Shugaban Ƙasar Nijar, Janar Abdulrahman Tchani, su suka fi faranta masa rai.
Muna roƙon Allah ya ji ƙan shi da rahama, ya sa ya huta. Mu kuma da muke nan, Allah ya kyautata tamu mutuwar, idan lokacinmu ya zo. Amin-Summa-Amin.
_______________













