• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Thursday, January 22, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Gumbar Dutse

Jinjina Da Yabo Ga Nagartaccen Shugaba: Malam Labiru Musa Ƙafur, mni

GUMBAR DUTSE

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
October 29, 2025
in Gumbar Dutse
0
Jinjina Da Yabo Ga Nagartaccen Shugaba: Malam Labiru Musa Ƙafur, mni

Wazirin Ɗangaladiman Katsina, Malam Labiru Musa Ƙafur,mni

5
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Jinjina Da Yabo Ga Nagartaccen Shugaba: Malam Labiru Musa Ƙafur, mni

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

MAGAJI GALADIMA: Yau Ne Maulidin Magayaƙin Kano

MAGAJI GALADIMA: Yau Ne Maulidin Magayaƙin Kano

September 29, 2023
Ashe Shaikh Jafar Mahmud Adam Bai Mutu Ba?

Ashe Shaikh Jafar Mahmud Adam Bai Mutu Ba?

May 29, 2023
Wazirin Ɗangaladiman Katsina, Malam Labiru Musa Ƙafur,mni

 

                       _______________

A yau muna taya murna da fatan alheri bisa rayuwar haziƙi, ɗan ƙasa, malami, kuma gogaggen ma’aikaci; Malam Labiru Musa Ƙafur, mni, wanda a yau ce daidai da ranar haihuwarsa.

An haifi Malam Labiru a ranar 28 ga Oktoba, 1954, a Ƙafur, Jihar Katsina. Rayuwarsa ta kasance abin koyi ga kowa. Ya kasance malamin makaranta mai jajircewa, har zuwa inda ya zama Babban Sakatare. Daga bisani kuma ya zama mamba na Cibiyar Nazarin Hikima da Dabaru ta Ƙasa (mni). Tarihinsa ya zama haske da ƙwarin gwiwa ga matasa da tsofaffi.

Malam Labiru ya fara karatunsa a Ƙafur Primary School (1961–1967), daga nan ya wuce Government Secondary School, Malumfashi (1968–1972). Sha’awarsa ta ilimi ta kai shi School of Basic Studies, Jami’ar Ahmadu Bello, Zaria (1973–1974), inda daga bisani ya sami digirin BA da M.Ed. Domin ƙara ƙwarewa a harkokin gudanarwa, ya halarci Administrative Staff College of Nigeria, Badagry (1991), sannan daga baya ya halarci National Institute for Policy and Strategic Studies, Kuru, Jos (1998), inda aka ba shi lambar girmamawa ta mni.

A rayuwar aiki, Alhaji Labiru Musa Ƙafur ya shahara wajen nuna ƙwazo, gaskiya da sadaukarwa. Ya fara aiki a matsayin malamin makaranta, sannan ya zama Senior Deputy Registrar (Academic) a Katsina Polytechnic (1986–1989). Daga nan ya riƙe muƙamai da dama a ƙananan hukumomi da ma’aikatun gwamnati, inda ya kasance Kantoma na Ƙaramar Hukumar Kurfi (1992), kuma daga baya ya zama Babban Sakatare (Permanent Secretary) a ma’aikatun Bayanai, Kuɗi Kasuwanci, kafin ya koma Ma’aikatar Kula da Ma’aikata (Civil Service Commission). Malam Labiru, shi ne Wazirin Ɗangaladiman Katsina.

A rayuwarsa, Allah ya yi wa Malam Kabiru baiwa da yawa. Yana da hali nagari da dabi’u masu kyau. Abokan aikinsa suna bayyana shi a matsayin mutum mai tawali’u, natsuwa, da sauƙin kai. Ba ya jagoranci cikin izza da ɗagawa, sai dai da shi shugaba ne mai nuna misali cikin nagarta da ƙwarewa. Dalili ke nan ake girmama shi, domin shi mutum ne mai hikima kuma mai adalci. Mutum ne da yake sauraron kowa cikin nutsuwa, abin da ke nuna zurfin tunani da basirar jagoranci.

Malam Labiru mutum ne mai tsoron Allah kuma mai ibada. Yana rayuwa cikin gaskiya da biyayya ga ƙa’idojin addini. Al’umma suna ganin shi a matsayin mai aminci kuma amintacce, wanda bai cika surutu da hayaniya ba. Duk da manyan muƙamansa, bai taɓa nuna girman kai ba; yana mu’amala da kowa da mutunci da tausayi. Shi mutum ne mai yawan taimako da kyauta, yana tallafa wa marasa ƙarfi da masu buƙata ba tare da neman yabo ba.

A matsayinsa na Matallafin Ƙungiyar Cigaban Ƙafur (Kafur Development Union), Malam Labiru ya sadaukar da lokacinsa da dukiyarsa wajen bunƙasa garinsu da taimakon jama’arsa. Son da yake yi wa ci gaban al’umma, ilimi, da ɗorewar matasa yana nuna cewa a wurinsa, jagoranci ba muƙami ba ne kawai, aiki ne na amana da kulawa. Ta hannunsa, mutane da dama sun sami shiriya da nasara a rayuwa.

A wannan rana mai albarka, muna taya shi murna tare da iyalansa, abokansa, da jama’ar Katsina baki ɗaya. Allah Ya ƙara masa lafiya, hikima, amibci da tsawon rai mai albarka. Rayuwarsa tana tuna mana cewa girma na gaskiya ba a cikin kuɗi ko iko yake ba, yana cikin yin hidima ga mutane da gaskiya, tausayi da tawali’u. Barka da zagayowar ranar haihuwa, Malam Labiru Musa Ƙafur, mni!
________________

Previous Post

Happy Birthday Sir: A Tribute to Malam Labiru Musa Ƙafur

Next Post

Daura Gidan Tarihin Hausa

Related Posts

MAGAJI GALADIMA: Yau Ne Maulidin Magayaƙin Kano
Gumbar Dutse

MAGAJI GALADIMA: Yau Ne Maulidin Magayaƙin Kano

September 29, 2023
Ashe Shaikh Jafar Mahmud Adam Bai Mutu Ba?
Gumbar Dutse

Ashe Shaikh Jafar Mahmud Adam Bai Mutu Ba?

May 29, 2023
Next Post
Daura Gidan Tarihin Hausa

Daura Gidan Tarihin Hausa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Tsakanin A’isha Humaira da Umar Baana: Sulhu Alheri Ne

Tsakanin A’isha Humaira da Umar Baana: Sulhu Alheri Ne

October 31, 2025
CANJIN ZAMANI: Rayuwar Mata A Ƙarni Na 21

CANJIN ZAMANI: Rayuwar Mata A Ƙarni Na 21

January 7, 2025
Koyaushe Talakka Zai Fita Daga Ƙuƙumi?

Koyaushe Talakka Zai Fita Daga Ƙuƙumi?

June 2, 2023
Nigeria at 64: How Far So Far?

Nigeria at 64: How Far So Far?

October 7, 2024

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (1)
  • Cikar Shekaru 83 A Duniya: Ranar Da Na Ga Zumunci Da Fatan Alheri Daga Masoya
  • Nazari, Tsokaci Da Sharhin Littafin Tarkon Mut’a

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (1)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (1)

January 21, 2026
My 83rd Birthday and the Kindred Spirit

Cikar Shekaru 83 A Duniya: Ranar Da Na Ga Zumunci Da Fatan Alheri Daga Masoya

January 19, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.