TARON MALUMFASHI FACEBOOK CONNECT: YUNKURIN BUNƘASA CIGABAN MALUMFASHI DA KEWAYE (1)
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

√ Gabatarwa:
Da sunan Allah mai rahama, mai jin ƙai. Tsira da aminci su tabbata ga fiyayyen halitta, manzon tsira, Annabi Muhammadu (saw).
Bayan haka, wannan bunƙasashen rahoto zai zo ne a sigogi mabambanta. Zai kasance a sigar labari, muƙala, sharhi da tsokaci, dangane da Ƙaramar Hukumar Malumfashi da al’ummarta, musamman ma dangane da kyakkyawan yunƙurin da matasa da shugabanni da malaman addini da attajiri da ‘yan siyasa da ‘yan kasuwa da ma’aikata suke gabatarwa ta fuskar bunƙasa yankin da al’ummarsa.
√ Yunkurin Matasa:
A kan haka, aka samu samu zaƙaƙuran matasa suka yunkuri da nufin kafa sabuwar tafiya mai manufa. Tafiyar da za ta zama tsani ko kuma ingizau, wajen samar da dauwamammen cigaba a Malumfashi da kewaye. Waɗannan matasa, sun yi amfani da faffaɗar kafar sadarwa ta soshalmidiya, domin cin ma wannan babban ƙuduri.
Matasan masu kishi na garin Malumfashi, sun yi nasarar shirya gagarumin taro, a ranar Lahadi 12-12-1446 (Hijiriyya), 08-06-2025 (Miladiyya); inda aka samu halartar kusan duk wasu masu ruwa da tsaki ko wakilansu a cikin al’umma. Rukunnan mutanen sun haɗa da sarakai, masu mulki, attajirai, ma’aikata, jami’an tsaro da matasa maza da mata.
√ Taro Ya Yi Armashi:
Taron, wanda ya gudana lami lafiya, an kira shi da sunan Malumfashi Facebook Connect, tare da taken “Mu Haɗu, Mu Gana, Domin Tafiya Tare Kuma Mu Tsira Tare.” Masana sun baje kolinsu, ‘yan siyasa sun baza haja, shugabanni sun ba da jagora, kamar kuma yadda makaɗa da mawaƙa suka nishaɗantar.

√ An Karrama Hadiman Al’umma:
Wani babban abin burgewa da yabawa da wannan taron shi ne, yadda aka zaƙulo wasu jajirtattu kuma nagartattun mutane da suke hudimta wa al’umma, aka karrama su da kambin yabo. Wannan zai ƙara masu ƙaimi da himma, domin su ci gaba da wannan aiki na gina al’umma.
Wasu daga cikin waɗanda aka karrama sun haɗa da Injiniya Muntari Sagir, Alhaji Jibrin Sama’ila (Jibson), Injiniya Tukur Tingilin, Malam Haruna Musa Rugoji, Dokta Bala Shehu da Kabir Malumfashi (KB Lamah).
Sauran sun haɗa da Abdulrahim Sallau Maƙauraci, Ɗandattijo Karfi, CSP Bello, DPO na Malumfashi, Alhaji Sanusi Maiwada, Babangida Usman Hada da Alhaji Yakubu Wada da kuma sauransu. (A rahotannin da za su biyo baya, za mu bi su ɗaya bayan ɗaya, mu zayyano irin ƙoƙarinsu da gudunmawar da suke ba al’ummar Malumfashi da kewaye).
√ Jagororin Shirya Taron:
Shin su wane ne jajirtattun matasa kuma ƙashin bayan shirya wannan taro mai albarka? Malam Yahaya Bawa, shi ne Shugaba, a yayin da Malam Isma’il DD ne Sakataren; sai kuma Malam Jibril Aliyu Datti, a matsayin Sakatare na biyu. Malam Mas’ud Sagir shi ne Ma’aji, inda shi kuma Malam Umar Maihaja ya kasance Shugaban Tsare-Tsare. Akwai Abdul’aziz Sardaunan Matasan Galadima, wanda shi ne Shugaban Gudanarwa da Walwala. Shi kuwa Abdullahi Saleesu, shi ne Jami’in Hulɗa da Jama’a. Haka kuma Ambasada Ibrahim Jaji, shi ne Jami’i Mai Gabatar da Taro.

Babu shakka, waɗannan mutane sun cancanci yabo, musamman yadda suka yi tsayin daka domin ganin taron ya tabbata cikin lumana, da kuma ganin cewa taron shi ne irinsa na farko a garin Malumfashi. Muna fatan a baɗi, idan Allah ya kai mu, za a samu babbar nasarar taron fiye da na bana.
A tarbi rahoto na gaba, domin ci gaba da kawo bayanai da sharhin yadda taron na bana ya gudana dalla-dalla, jawabai, mukaloli da ƙasidun da aka karanta a yayin taron.
_______________
Bashir Malumfashi, shi ne Editan Mujallar Taskar Gizago (online)














Masha Allah,Allah yakara hada kayunanmu domin cigaban garinmu me albarka malumfashi dakuma wannan jarida ta taskargizago domin tana wayarda kan’al’umma tabangarori dayawa Allah yaqara jagoranci yayanmu Bishir Yahuza malumfashi.Inama kowa fatan alkhairi
Ma sha Allah. Muna matukar godiya da wannan kwarin gwiwa da aka ba mu. Allah saka da alheri. Wasallam.