TSOKACINMU NA YAU (20)
Yau Alhamis, 20-Ramadan-1446, Hijirar Manzon Allah (saw), wacce ta yi daidai da 20-Maris-2025, Miladiyya.
A yau za mu yi wa juna tambihi ne, watau mu zama masu tsinkaye a dukkan abin da za mu aikata. Nasiharmu ita ce, mu fahimta da cewa, duk abin da muka aikata a rayuwa yana da sakamako; wanda komai daɗewar lokaci zai dawo gare mu.
Idan muka aikata aikin alheri, babu shakka shi zai dawo mana, haka ma akasinsa. Masu hikima sun ce, alheri danko ne, ba ya faɗuwa ƙasa banza. Kamar kuma yadda suka ce, mugunta fitsarin faƙo ce, mai ita take ɓatawa. Don haka, mu kiyaye.
Allah sa mu dace, Amin.
Mu wuni lafiya.
Naku,
Bashir Yahuza Malumfashi,
Editan Mujallar Taskar Gizago.













