TSOKACINMU NA YAU (18)
Yau Talata, 18-Ramadan-1446, Hijirar Manzon Allah (saw), wacce ta yi daidai da 18-Maris-2025, Miladiyya.
Kishin Ƙasa: Wannan shi ne taken tsokacinmu na yau. Kishin ƙasa yana nufin kowane ɗan ƙasa ya amince kuma ya ƙudurce a zuciyarsa cewa, babu wata ƙasa a duniya da ta kai kasarsa ta haihuwa.
Ɗan ƙasa zai nuna haka kuma a aikace. Ya zama mai yin duk wani abu da zai bunƙasa ƙima da martabar ƙasarsa, kamar bin doka da oda, gudanar da aikinsa ko sana’arsa bisa dacewa da ɗa’a da kuma guje wa duk wata halayya da za ta kawo wa ƙasarsa rasa daraja da muhibba.
Wannan shi ne kishin ƙasa kuma kowane ɗan ƙasa ana son ya haɗa hannu da sauran ‘yan ƙasa, domin yi mata hidima, domin ta samu bunƙasa da ci gaba.
Allah sa mu dace, Agem, min.
Mu wuni lafiya.
Naku,
Bashir Yahuza Malumfashi,
Editan Mujallar Taskar Gizago.













