TSOKACINMU NA YAU (07)
Yau Juma’a, 07-Ramadan-1446, Hijirar Manzon Allah (saw), wacce ta yi daidai da 07-Maris-2025, Miladiyya.
Ga tsokacinmu na yau:
“Ya ku ‘yan uwa, yau tsokacinmu zai fuskanci al’amari mafi muhimmanci a rayuwa, watau ILIMI. Tabbas, ilimi ba kawai shi ne gishirin zaman duniya ba, shi ne ma babban ginshiƙin dukkan nasarar rayuwar duniya da lahira.
Muhimmancin ilimi ya wuce duk tunanin mai tunani, domin kuwa idan mun lura, sakon farko da Allah Ya aiko zuwa ga fiyayyen talikai, Annabi Muhammadu (saw), shi ne karatu, watau ilimi.
Saboda haka, duk mai son nasara a rayuwa, to ya jajirce ya nemi ilimi. Mutum ya kasance mai karatu da karatu da karatu. Mu kasance masu ɗabi’ar karanta littattafai masu muhimmanci, ba na sharholiya da shiririta ba.”
Allah sa mu dace, Amin.
Mu wuni lafiya.
Naku,
Bashir Yahuza Malumfashi,
Editan Mujallar Taskar Gizago.













