TSOKACINMU NA YAU (03)
Yau Litinin, 03-Ramadan-1446, Hijirar Manzon Allah (saw), wacce ta yi daidai da 03-Maris-2025 Miladiyya.
Ga tsokacinmu na yau:
“Ya ku ‘yan uwa, mu sani cewa, mu sani cewa, a kowace zamantakewa, babu abin da ya kai muhimmancin ‘haɗin kai.’
Da haɗin kai ne ake iya tunkarar kowace irin matsala kuma a ga bayanta. Masu iya magana sun ce, haɗin kai shi ne ƙarfi. Don haka, a tsakanin iyali, wurin aiki, unguwa, gari ko jiha, da ma ƙasa baki ɗaya, muna buƙatar haɗin kai domin samun nasara.”
Allah sa mu dace, Amin.
Mu wuni lafiya.
Naku,
Bashir Yahuza Malumfashi,
Editan Mujallar Taskar Gizago.













