ABDULLAHI ALKWATONAWI: ALLAH JI ƘAN ƊAN UWA DA RAHAMA

•••
Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un!
A jiya Laraba – 13-08-1446 = 12-02-2025 da maraice, Shugaban Ƙungiyar Gizago ta Najeriya, Malam Muhammad Kabir MK Adam Gombe ya sanar da ni labarin rasuwar ɗaya daga cikin manyan shugabannin ƙungiyar, Malam Abdullahi Alkwatonawi, wanda dama yake cikin doguwar jinya, kafin rasuwar tasa.
Marigayin, ɗan asalin Jihar Kano ne, wanda ya yi zama a Legas, inda ya riƙa gudanar da harkokinsa na neman abinci.
A can Legas ɗin, marigayin ya riƙe muƙamai da dama a Ƙungiyar Gizago, kama tun daga Shugaban Gizagawan Jihar Legas, zuwa Mataimakin Shugaban Kungiya na Ƙasa da kuma Ma’ajin Ƙungiya na Ƙasa.
Marigayi Abdullahi mutum ne mai zumunci da ƙoƙarin hidima ga ‘ya’yan ƙungiya da ƙoƙari da tsayin daka wajen inganta zumunta a cikin ƙungiya.
A madadin ni kaina, Bashir Yahuza Malumfashi, Fasihin Galadiman Katsina-I da iyalina, ina miƙa gaisuwar ta’aziyya ga iyalansa da ɗaukacin Gizagawan Zumunci, ‘yan uwa da abokan arziƙi.
A yadda kafin rasuwarsa ya sha jinya, muna rokon Allah Ya sa ta zama kaffara a gare shi. Muna roƙon Allah Ya ji ƙan shi da rahama.
AMIN-SUMMA-AMIN
•••













