ABIN DA YA SA AKE RAINA MAGANAR WASU “MALAMAI”

√ GABATARWA:
Babu shakka Allah Ya karrama malamai kuma ya yabe su sosai a wurare da yawa a cikin littafinSa mai girma (Alkur’ani). Sai dai kuma ba kowane malami ne ya cancanci yabo da karramawa ba, sai MALAMIN ALLAH, wato “auliya’ullahi” wanda Allah Ya yi wa alƙawarin: “laa khaufun alaihim walahum yahzanun.” Wannan yake nuna cewa ke nan akwai gurɓatattun malamai, masu ci-da-ceto, waɗanda ko kaɗan ba za su samu irin waccan karramawar daga Allah ba. A wannan taƙaitaccen tsokacin, zan bayyana wasu ‘yan dalilai ƙalilan da suka sanya al’umma ke wa wasu “malamai” gani-gani a wannan zamani. A gani na, ga kaɗan daga cikin dalilan:
~~~
1 √ Malaman baya da suka yi shuhura, kamar Sheikh Gumi, Ja’afar Mahmud Adam, Albany Zaria suna da tawali’u da gudun duniya. Ba su yin tarayya da masu mulkin da suke zaluntar al’umma, balle su riƙa ba su kariya.
2 √ Su kuwa wasu daga fitattun malaman wannan zamanin, har rige-rige suke wajen ba azzaluman masu mulki kariya.
3 √ Marigayi Sheikh Gumi ya yi rayuwar Zuhudu, bai tara dukiyar haram ba. Har ya mutu suturunsa ƙidayayyu ne. Bai da gida a Abuja ko Legas, bai da babbar motar kece raini.
4 √ Malaman yanzu sun tsunduma ga son duniya da ƙyaleƙyalenta. Su ne da manyan suturun kece raini. Su ne da shiga manyan mitoci cikin ayari kamar gwamnoni. Su ne da manyan gidaje a manyan birane. Alhali mabiyansu suna cikin talauci da buƙata.
5 √ Marigayi Sheikh Mahmud Gumi, a duk lokacin da aka kawo masa zakka, komai yawan ta, a nan take yake rarraba wa almajiransa da suke da buƙata.
6 √ Wasu manyan malaman yanzu kuwa, daga mabiyansu suke tara dukiya. Ko dai su sallamar da mabiyansu ga ‘yan siyasa ko kuma su riƙa tattara sadakar da ake bayarwa domin amfanin kansu. Ko makaranta suka gina, ɗan talaka ba zai iya karatu a cikinta ba saboda tsadar kuɗin makaranta da suke sakawa.
7 √ Marigayi Sheikh Ja’afar ya kasance mai fayyace gaskiya ga masu mulki, kamar yadda yake faɗakarwa ba tare da kare wata ƙungiyar addini ba. A matsayinsa na ɗan Ƙungiyar Izalatul Bid’a wa Iƙamatussunna, ko ita ta kauce hanya, yana bayyanawa tare da neman a gyara. A lokacin da gwamnati ta ba shi shugabancin Hukumar Hizba ta Jihar Kano, da ya gano cewa ba da gaske ake ba wajen tabbatar da gaskiya, sai ya aje muƙamin, domin abin ya yi karo da aƙidarsa ta jaddada gaskiya da son kawo gyara.
8 √ Marigayi Sheikh Albany Zaria ya kasance tsayayyen malami mai cin gashin kansa. Bai zama ci-ma-zaune ba, wanda ke jiran ɓarayin gwamnati su ba shi zakka ko sadaka ba. Sana’a yake yi sosai kuma yake sadaukar da abin da ya samu wajen gina makarantu da wallafe-wallafe domin karantar da mabiyansa da ‘ya’yansu.
9 √ Ke nan babban abin da zai sa a riƙa daraja malami kuma a riƙa sauraren maganganunsa shi ne, ya nuna da gaske yake kan da’awarsa. Ya kasance mai tausayi da jin ƙan mabiyansa.
10 √ Ya kamata malamai su tsaya a matsayinsu na gaskiya da gaskiya – magada annabawan Allah. Su tsaya kan gaskiyar koyarwa bisa Igiyar Allah. Su daina haifar da rarraba kan al’umma da sunan ƙungiyanci. Su zamanto masu son al’umma da kishin su na gaskiya.
~~~














ABIN DA YA SA AKE RAINA MAGANAR WASU “MALAMAI” – Taskar Gizago
aydjyedih
ydjyedih http://www.g28c87jwqd0e6tn7577l28030vmgp5ohs.org/
[url=http://www.g28c87jwqd0e6tn7577l28030vmgp5ohs.org/]uydjyedih[/url]