YAU 40: ALLAH YA JI ƘAN HAJIYA ZAINAB AHMAD

A yau ne mahaifiyar Mansur Ahmad, Hajiya Zainab Ahmad ta cika kwanaki 40 da rasuwa.
A yayin da yake sanar da haka a shafinsa na Facebook, Malam Mansur ya yi addu’ar cewa:
“Muna roƙon Allah Ya yafe mata, Ya yalwata ƙabarinta, Ya jadadda rahama a gare ta, Ya saka mata dukkan ni’ima daga dausayin aljanna, Ya haɗa mu da ita a gidan aljanna maɗaukakiya; ita da mahaifinmu da dukkan Musulmi. In lokacinmu ya yi, Allah Ya sa mu cika da kyau da imani.
“Allah, duk wanda suke tare da iyayensu, Ka ba su ikon kyautata musu; Ka raba su da su lafiya in lokacin rabuwar su ya yi.
“Allah Ka ƙara mana haƙuri da juriya, Ka saka wa jama’a da alheri, na kasancewa tare samu a wannan waƙi’a.”
Amin Ya Allah.












