• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Friday, January 16, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Labarai

Gwamnatina Za Ta Mutunta ‘Yancin Kafafen Yaɗa Labarai

Za Ta Karɓi Yabo, Gyara Da Suka Daga 'Yan Jarida Da Marubuta - Tinubu

Daga Wakilinmu by Daga Wakilinmu
December 19, 2023
in Labarai
0
Gwamnatina Za Ta Mutunta ‘Yancin Kafafen Yaɗa Labarai

Shugaba Tinubu yana jawabi ga mawallafa jaridu

11
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Gwamnatina Za Ta Mutunta ‘Yancin Kafafen Yaɗa Labarai

* Za Ta Karɓi Yabo, Gyara Da Suka Daga ‘Yan Jarida Da Marubuta – Tinubu

Related posts

Bura women Celebrate Bukar Usman at 83

Ƙungiyar Matan Al’ummar Bura Sun Karrama Dr. Bukar Usman Bisa Cika Shekaru 83

January 9, 2026
Sojoji Sun Ƙwato Muggan Makamai A Jihar Taraba

Sojoji Sun Ƙwato Muggan Makamai A Jihar Taraba

January 5, 2026

Shugaba Bola Tinubu ya ƙara jaddada cewa gwamnatin sa a ko yaushe za ta mutunta ‘yancin kafafen yaɗa labarai da ‘yan jarida, kuma za ta yi maraba hannu biyu da ra’ayoyin masu nuni da yin gyara, suka ko yabon gwamnatinsa.

Cikin sanarwar da Kakakin Yaɗa Labaran Shugaban Ƙasa, Ajuri Ngelale ya fitar, ya ce Tinubu ya yi wannan bayani ranar Litinin, lokacin da ya gana da mambobin Ƙungiyar Mawallafa Jaridu ta Nijeriya (NPAN).

Shugaba Tinubu ya tabbatar masu da cewa zai zauna a tsanake ya duba buƙatar da suka bijiro masa da ita, wato ta neman a sassauta tsarin hada-hadar takardar buga jarida, wanda ke ci wa gidajen jaridu tuwo a ƙwarya ta hanyar tsadar takardun a cikin gida.

Da ya koma kan wahalhalun da matafiya ke fuskanta a yanzu lokacin tafiya hutun Kirsimeti da sabuwar shekara, Shugaba Tinubu ya ce gwamnatin tarayya za ta ɗauki matakan sauƙaƙa tsadar zirga-zirga da sufurin jiragen sama, na ƙasa da kuma kan titinan motoci.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris ne ya jagoranci tawagar masu gidajen jaridun a wannan ziyarar da suka kai wa Shugaba Tinubu.

Shugaban ya ci gaba da cewa ana nan ana ɗaukar matakan da za a rage farashin gas.

“Na damu sosai dangane da abin da ke faruwa a cikin ƙasar nan. Ina gode maku kan goyon bayan da ku ke bayarwa da ra’ayoyi da sukar da ake yi wa gwamnatin mu. Ba domin goyon bayan wasu daga cikin ku ba, ba zan zama shugaban ƙasa ba, har ga ni a yanzu tare da ku a matsayin shugaba.

“Kun jajirce kan aikin ku cikin rintsi da tsanani. Don haka mu kuma za mu ci gaba da mutunta ra’ayoyin ku, ko da kuwa ba mu yarda da abin da ku ka faɗa kan mu ba.

“Abu ɗaya da zan faɗa maku shi ne, ina karanta kowace jarida, ina kuma karanta ra’ayoyin da ake rubutawa, har ma da shafukan manazarta da marubuta ra’ayoyi daban-daban,” inji Tinubu.

A jawabin sa, Ministan Yaɗa da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jaddada kyakkyawar aniyar Gwamnatin Tarayya ta shata wa kafafen yaɗa labarai kyakkyawar shimfiɗa a ƙasar nan.

“Dimokraɗiyyar mu ta ginu ne a kan tsari da tafarkin ƙa’ida da tabbatar da komai bisa kyakkyawan tsarin doka da kuma ‘yancin yaɗa labarai da bayanai.

“Rawar da kafafen yaɗa labarai musamman jaridu ke bayarwa ta na da tasiri da muhimmanci a wannan turbar dimokraɗiyya,” cewar Minista Idris.

Daga nan Idris ya jinjina wa jagororin NPAN saboda samar da ƙungiya mai ƙarfin tattauna batutuwan da suka shafi ƙasa da kuma bayar da damar sauraren muryoyin jama’a mabambanta ra’ayoyi da fahimta.

Shi kuma Shugaban NPAN, kuma shugaban kamfanin Media Trust, masu buga Daily Trust, Trust TV da Aminiya, Malam Kabiru Yusuf, ya fara da yi wa Shugaba Tinubu murnar nasarar zaɓe da kuma nasara a Kotun Ƙoli. Daga nan ya ci gaba da lissafo matsalolin da suka dabaibaye masana’antu da hada-hadar takardar buga jaridu.

Previous Post

Jami’ar Bayero Ta Karrama Janar Buratai

Next Post

INEC Za Ta Gudanar Da Zaɓuɓɓukan Da Kotu Ta Soke Da Na Cike Gurabu 34 A Fabrairu 2024 – Yakubu

Related Posts

Bura women Celebrate Bukar Usman at 83
Labarai

Ƙungiyar Matan Al’ummar Bura Sun Karrama Dr. Bukar Usman Bisa Cika Shekaru 83

January 9, 2026
Sojoji Sun Ƙwato Muggan Makamai A Jihar Taraba
Labarai

Sojoji Sun Ƙwato Muggan Makamai A Jihar Taraba

January 5, 2026
Hukuncin Nnamdi Kanu: Minista Bianca ta Nemi Igbo Su Guji Tada Fitina
Labarai

Hukuncin Nnamdi Kanu: Minista Bianca ta Nemi Igbo Su Guji Tada Fitina

November 22, 2025
Next Post
Zaɓen gwamna: Mutum 2,318,919 za su yi zaɓe a Imo, 1,833,160 a Kogi, 1,017,613 a Bayelsa, inji INEC

INEC Za Ta Gudanar Da Zaɓuɓɓukan Da Kotu Ta Soke Da Na Cike Gurabu 34 A Fabrairu 2024 - Yakubu

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

GOBARA DAGA KOGI: ‘Yan Bindiga Sun Farmaki Fadar Gwamnatin Amurka

GOBARA DAGA KOGI: ‘Yan Bindiga Sun Farmaki Fadar Gwamnatin Amurka

November 27, 2025
GENERAL BURATAI PAYS HOMAGE TO GENERAL BUHARI

GENERAL BURATAI PAYS HOMAGE TO GENERAL BUHARI

March 9, 2025
IDAN APC TA AMSHI KANO: INA MAKOMAR SARAKUNA BIYU?

IDAN APC TA AMSHI KANO: INA MAKOMAR SARAKUNA BIYU?

April 17, 2025
Rusau A Kano: An Fara Kama Ɓarayin Kayan Mutane

Rusau A Kano: An Fara Kama Ɓarayin Kayan Mutane

June 5, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation
  • Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco
  • Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

January 15, 2026
Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

January 14, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.