Jami’ar Bayero Ta Karrama Janar Buratai
Shi Kuma Ya Ba Jami’ar Kyautar Littafin Tarihinsa
Jami’ar Bayero Kano ta karrama Laftanar-Janar Tukur Yusufu Buratai, CFR (mai ritaya) da Kambin Girmamawa, a matsayinsa na ɗaya daga cikin jakadun Najeriya da suka kare martabar ƙasarsu a ƙasashen waje.
Janar Buratai, wanda shi ne tsohon Hafsan-Hafsoshin Rundunar Sojojin Najeriya kuma tsohon Jakadan Najeriya a Jamhuriyar Benin, Betaran Biu kuma Garkuwan Keffi, an karrama shi ne a yayin taron ƙara wa juna ilimi da Tsangayar Nazarin Jinsuna) (Center For Gender Studies) da ke Jami’ar Bayero Kano ta shirya.
Taron na kwana biyu, mai taken “Inganta Ilimin Matasa Domin Samun Kyakkyawar Rayuwa” ya gudana ne a jiya Juma’a (15-12-2023) a babban zauren taro na jami’ar da misalin ƙarfe goma na safe. Kuma an karrama shi ne bisa la’akari da irin gudunmowar da yake bai wa al’umma, musamman matasa maza da mata, domin inganta rayuwarsu.
A yayin gabatar da jawabinsa, Betaran Biu, ya miƙa godiyarsa ta musamman ga wannan tsangaya da ta shirya taron. Haka kuma ya yaba mata, bisa himmarta wajen horar da ƙwararrun mutane kuma ingattatu a fannoni daban-daban, domin samar da kyakkyawan ci gaba ga kansu da ƙasarsu baki ɗaya.
Haka kuma ya yi jinjina ga masanin Shari’a, Farfesa Auwalu Yadudu, wanda ya ce abokinsa ne mai ƙwazon yi wa al’umma hidima.
“Wajibi ne in miƙa godiya ta musamman ga abokina, wanda duk da cewa ya yi ritaya amma ba ya gajiya wajen yi wa al’umma hidima. Ga shi kuma ya halarci wannan taro. Muna ƙara yi maka barka da zuwa,” in ji Janar Buratai.
Haka kuma, bayan an karrama Garkuwan na Keffi da Kambin Girmamawa, shi kuma ya bai wa Sashin Nazarin Harsuna na Jami’ar ta Bayero kyautar littafin tarihin rayuwarsa da gwagwarmayarsa, mai taken HIKIYAR JARUMI BURATAI) na 1 da na 2, wanda Malam Bashir Yahuza Malumfashi ya wallafa kuma ake shirin ƙaddamarwa nan gaba.
Yayin da yake miƙa littattafan ga Shugaban Jami’ar, Farfesa Sagir Adamu Abbas, Janar Buratai ya ce, “wannan na daga kaɗan daga gudunmowar da muke son bayarwa wajen bunƙasa harsunan gida, ta yadda cibiyar za ta ƙara haɓaka tare da gogar da matasa musamman a ɓangarori daban-daban, ta yadda za a kawo ci gaban ƙasa a harkokin tsaro da samar da ingantaccen ilimi, wanda kuma shi ne babban ƙalubale.”
Ya ƙara da cewa, “tun jiya ina cikin garin Kano. Na ga yadda suke da ɗimbin matasa da ke bisa hanyoyi. Na lura da cewa akwai ƙalubale a ɓangaren tattalin arziki saboda haka waɗannan matasa ku da kuka samu wannan horo, ku jajirce wajan tsamo ‘yan uwanku daga matsalolin rayuwa.
“Ina taya ku murna da kuka samu wannan ilimi. A ƙarshe, ina fatan idan kun fita daga wannan makaranta, za ku yi ƙoƙarin ɗabbaƙa abun da kuka koya a aikace. Ina gode muku baki ɗaya da dukkanin mahalarta.
Taron ya samu halartar manyan malamai da jami’an gwamnati masu ci da tsofaffi


bisa shugabancin Farfesa Sagir Adamu Abbas, Shugaban Jami’ar Bayero da Farfesa Ruƙayya Ahmad Rufa’i, tsohuwar Ministar Ilimi da Dokta Suwaiba Sa’id Daraktar Tsangayar Nazarin Jinsuna ta jami’ar (CGS). Akwai kuma Alhaji Ahmad Rabi’u Ahmad da Dokta Manzo Ahmad.
Sauran sun haɗa da Farfesa Auwalu Yadudu da Farfesa Muhammad Yahuza Bello da Farfesa Mukhtar Atiku Kurawa, Shugaban Jami’ar Yusuf Maitama Sule da Alhaji Adamu Muhammad Buratai da sauransu da dama daga sassa daban-daban na ƙasar nan.













