DARASIN JUMU’A SHEIKH GAMAWA
Daga Sheikh Aliyu Said Gamawa
~~~~~~~
Ya kai ɗan Adam ka sani, arziƙin kowa a hannun Allah yake. Kuma babu wani wanda ya isa ya riƙe arziƙin wani ko ya ƙara masa, sai Allah Ya so.
Ya kai bawan Allah ka sani, babu mai tsaya maka a kan ayyukanka. Don haka ka shagaltu da kanka, ka yi ta ayyukan alheri don gobe ƙiyama.
Ya ku al’umma, tabbas a ko’ina muke, ALLAH Yana kallon mu. Tuna hakan zai sa bawa ya ji kunyar Allah yana jin sa yana ganin sa. Don Allah mu guji ɓuya muna aikata saɓo.
Lallai ne mu sani, haƙiƙa MUTUWA na jiran kowa. Don haka mu dage wajen tanadin guzurin haɗuwar mu da Ubangiji ranar hisabi.
~~~~~~~












