Huɗubar Jumu’a A Taƙaice Daga Masallacin Dr. Yunusa Zuba-Abuja
A yau Juma’a, 17-01-1445 (Hijriyya), 04-08-2023, Limamin Masallacin Dokta Yunusa da ke garin Zuba, Babban Birnin Tarayya Abuja, Liman ya buɗe huɗubarsa da basmala da godiya ga Allah da salati da sallama ga Manzon Allah, Sallallahu alaihi Wasallam.
Maudu’in huɗubar ya karkata ne zuwa ga yanayin ƙunci da wahala da talauci da tsananin rayuwa da al’umma ke ciki. Malam ya jawo hankalin al’umma da mu fahimci yanayin da ake ciki na tsadar rayuwa, inda wasu ke kwana da yunwa kuma su tashi da yunwa. Mutane na fuskantar barazanar talauci. Ga marasa lafiya kuma ba su da abin sayen magani.
Malam ya buƙaci al’umma da mu kasance masu taimakon juna. Ya ce kowa ya kalli na kusa da shi, ya taimaka wa wanda yake da buƙata da abin da Allah Ya hore masa, komai ƙanƙantarsa.
Malam Ya ce akwai fa’ida sosai a taimakon mabuƙaci. Mu kasance masu ƙoƙarin yaye wa ‘yan uwanmu wata damuwa da suke ciki. Kuma mu sani, duk wanda ya cire wa ɗan uwansa wata damuwa, shi ma Allah zai cire masa tasa damuwar, duniya da lahira.
Malam ya nemi da mu kasance ‘yan uwan juna, mu kare haƙƙoƙin juna. Ya ce Musulmi ɗan uwan Musulmi ne, a lokacin da yake raye da kuma bayan mutuwarsa. A lokacin da yake raye, yana da haƙƙin ka kula da shi, ka taimake shi a lokacin da yake buƙatar taimako. A lokacin da ya mutu kuwa, yana da haƙƙin ka yi masa addu’a.
Malam ya kawo hadisin da ke ƙarfafa muhimmancin taimakon juna, wanda ke cewa lallai Allah yana taimakon bawa, madamar bawa yana taimakon ɗan uwansa.
“Duk wanda ke son dacewa a duniya da lahira, to ya lizimci taimakon ɗan uwansa. Don haka mawadata su taimaka wa mabuƙata, Allah zai taimake su.
Malam Ya rufe huɗubarsa da addu’a, Allah Ya kawo mana sauƙi, Ya ba mu damina mai albarka.
Amin summa Amin!













