NASIHA
Ɗan uwa biɗi rayuwa
Amma fa kar ka yi hanzari.
Duniya ta yi kasuwa,
Sai dai ka zamto ƙoƙari.
Ka kiyayi aikin ɗimuwa,
Kai dai ka zam mai marmari.
Haƙƙinka ba ya samuwa,
Sai ka zamo mai haƙuri.
Ka zamto mai guje damuwa,
Zuciyar kan fita sasari.
Ubangiji Shi ke basuwa,
Sai ka bauta ba kakari.
Allah Ka sa mun datuwa,
Lamuranmu zamto nasari.
~~~~~~~
© Bashir Yahuza Malumfashi
An rubuta Waƙen Nan
Alhamis, 18-07-2019 (Miladiyya)
15 Zulƙida, 1440 (Hijiriyya)
~~~~~~~













