HAWAYEN RABUWA: LITTAFIN TA’AZIYYA DA ALHININ MARIGAYI AUWALU GARBA ƊANBORNO (24/12/78 – 25/6/2023)
Duniyar marubuta da ‘yan uwa da abokan arziki su shiga cikin ruɗu da kuma firgici na rasuwar ɗan uwanmu kuma abokinmu, Marigayi Auwalu Garba Ɗanborno wanda babban makusancinsa kuma amininsa (Dr.) Aminu Ladan Abubakar Alan Waƙa (Sarkin Ɗiyan Gobir) ya bayyana a baiton waƙa da cewa, Auwalu marubuci ne, Auwalu manazarci ne…”.
Da ya ke Marigayin mutum ne na mutane, tabbas duniyar soshal midiya ta cika da saƙonni na alhinin da jin labarin rashin wannnan babban zaƙaƙurin marubuci da manazarci wanda manomi ne kuma jam’in tsaro aboki ga kowa da kowa. Marigayi AG ya shahara wajen bayyana fahimtarsa ta hanyar tsage gaskiya komai dacinta. Mutum ne mai kishin addini da kishin mutanen Arewa a cikin rubuce -rubucensa wanda ya yi a wasu littattafai da shafinsa na Feskub a dandalin soshal midiya.
Don taskace kaɗan daga ire – iren wasu daga cikin gudunmawarsa ga raya al’umma da kuma wasu daga bayanan alhinin da ‘yan uwa da abokan arzikinsa suka bayyana game da rasuwarsa, babban amininsa (Dr.) Aminu Ladan Abubakar ya ƙuduri niyyar wallafa littafi don bayyanawa duniya cikkaken hoto shin wa ye Marigayi Auwalu Garba Ɗanborno.
Bisa wannan niyya ana gayyatar duk waɗanda suka rubuta waƙa ko wani bayani game da wannan ɗan uwa namu da su turo wannan bayani zuwa wannan akwatin imail:
danladiharuna#gmail.com.
ƘA’IDOJIN AIKO DA RUBUTU
1. A za iya aiko da waƙa ko gajeran labari ko saƙon ta’aziya amma wajibi ne ya zama ya shafi marigayi AG.
2. Tsawon waƙa kar ta wuce baitoci 35, Gajeran labari kar ya wuce kalmomi 1500 saƙo ta’aziya kuma kar ya gaza kalmomi 300 ko wuce kalmomi 500.
3. An buɗe karbar saƙonnin rubutu ne tun daga ranar 1 ga watan Juli, 2023.
4. Za a rufe karɓar saƙonin rubutu a ranar 14 ga watan Juli, 2023.
Sanarwa:
Khalid Imam
Shugaban Dandalin Muryar Adabi
A madadin:
Dr. Aminu Ladan Abubakar (Sarkin Ɗiyan Gobir).
Domin neman ƙarin bayani ko haske a iya tuntubar wannan lamba 08027796140












