• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Thursday, March 5, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Babban Labari

Ranar Dimokuraɗiyya: Mu Jajirce Wajen Gina Ƙasa – MD Abubakar

Shugaban Ƙungiyar Ɗaliban Kwalejin Dabarun Mulki ta Ƙasa

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
June 11, 2023
in Babban Labari
3
Ranar Dimokuraɗiyya: Mu Jajirce Wajen Gina Ƙasa – MD Abubakar

MD. Abubakar

38
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Shugaban Ƙungiyar Ɗaliban Kwalejin Dabarun Mulki ta Ƙasa (AANI), tsohon Sufeto-Janar na ‘yan sandan Najeriya, MD Abubakar, CFR, ya buƙaci al’ummar Najeriya da su yi amfani da Ranar Dimokuraɗiyya ta bana wajen haɗa kai da juna wajen gina ƙasa, domin tabbatar da zaman lafiya da bunƙasa tattalin arzikin ƙasa ba tare da nuna wariya ba.
Shugaban, a yayin da yake taya ‘yan Najeriya murnar zagayowar wannan rana ta dimokuraɗiyya, a wata takardar manema labarai da Sakataren Watsa Labaran ƙungiyar, Birgediya-Janar (mai ritaya), Sani Usman Kuka-Sheƙa ya sanya wa hannu, ya bayyana cewa:
“A yayin da muke murnar zagayowar Ranar Dimokuraɗiyya a yau 12 ga Yuni, 2023, lokaci ne da ya kamata mu waiwaya baya, a tarihin siyasar ƙasar nan, wanda ke ƙara nuna himma da jajircewar ‘yan Najeriya, na tabbatar da kafuwar kyakkyawan shugabancin dimokuraɗiyya mai ɗorewa.”
Ya jaddada cewa, tsarin dimokuraɗiyya ya ba ‘yan ƙasa damar bayyana ra’ayinsu, sannan ya ba su ‘yancin zaɓen shugabanninsu da kansu, domin ciyar da ƙasa gaba. “Tsari ne da yake ƙarfafa wa ‘yan ƙasa, su ba da tasu gudunmawa wajen gina ƙasa. Don haka a yayin da muka samu wannan sabuwar gwamnati, sai mu haɗa hannu a dama da mu wajen tabbatar da gudanuwar tsarin dimokuraɗiyya, musamman wajen tattaunawa mai ma’ana da yin aiki tare da juna wajen magance matsalolinmu da ƙalubalen da ke damun ƙasarmu,” in ji shi.
Da ya juya ga ‘yan ƙungiyar tasu ta AANI kuwa, Shugaba MD. Abubakar ya ja hankalinsu da cewa, a matsayinsu na shugabannin al’umma, ya kamata su riƙa nuna shugabanci na adalci bisa misali na ƙwarai. Kuma su riƙa ɗabbaka halayen ƙwarai na tafiya tare da al’umma cikin amana da gaskiya. “Muna ƙarfafa gwiwa ga duk wani tsari na ci gaban al’umma, wanda zai taimaka wajen samar da zaman lafiya da ci gaban ƙasa,” in ji shi.
Da ya juya kan jami’an tsaro kuwa, Shugaban Ƙungiyar Ɗaliban yaba masu ya yi, musamman saboda namijin ƙoƙarin da suke yi wajen kare al’ummar ƙasa da samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali ga al’umma. Don haka ya buƙaci ɗaukacin al’ummar ƙasa da su so juna, su haɗa kai domin gina ƙasa ba tare da nuna wariya da bambancin yare, ƙabila, yanki ko addini ba.
Ya ƙarƙare da addu’a ga Najeriya da al’ummarta baki ɗaya. “Ya Allah Ka sanya mana soyayyar juna, Ka ba mu haɗin kai da zaman lafiya. Ka yi mana jagora bisa hanyar ci gaba, Ka haskaka mana al’amura yadda gabanmu za ta yi kyau fiye da baya. Allah sa wannan dimokuraɗiyya ta zame mana alheri da ƙarfafa gwiwar ‘yan ƙasa domin samar da ci gaba mai ɗorewa a Najeriya.”

Related posts

Gwamnan Jigawa Ya Amso Walida Daga Hukumar DSS

Gwamnan Jigawa Ya Amso Walida Daga Hukumar DSS

February 26, 2026
Wata Mata Ta Haifi “Hatsabiban Jarirai” A Ofishin Hukumar NDLEA

Wata Mata Ta Haifi “Hatsabiban Jarirai” A Ofishin Hukumar NDLEA

February 22, 2026
Previous Post

Rusau A Kano: Ba A Gyara Kuskure Da Kuskure

Next Post

Ambaliya Ce Babbar Ƙalubalen Manoman Jigawa – Isa Billami

Related Posts

Gwamnan Jigawa Ya Amso Walida Daga Hukumar DSS
Babban Labari

Gwamnan Jigawa Ya Amso Walida Daga Hukumar DSS

February 26, 2026
Wata Mata Ta Haifi “Hatsabiban Jarirai” A Ofishin Hukumar NDLEA
Babban Labari

Wata Mata Ta Haifi “Hatsabiban Jarirai” A Ofishin Hukumar NDLEA

February 22, 2026
Musulmin Kudancin Najeriya Sun Jaddada Mubaya’a Ga Sarkin Musulmi
Babban Labari

Musulmin Kudancin Najeriya Sun Jaddada Mubaya’a Ga Sarkin Musulmi

February 13, 2026
Next Post
Ambaliya Ce Babbar Ƙalubalen Manoman Jigawa – Isa Billami

Ambaliya Ce Babbar Ƙalubalen Manoman Jigawa - Isa Billami

Comments 3

  1. Ibrahim Abubakar Wuriwa Hadejia says:
    3 years ago

    Ma Sha Allah. Allah ta’ala ya Kara haskaka jaridar GIZAGO

    Reply
    • Bashir Yahuza Malumfashi says:
      3 years ago

      Amin Amin Ya Allah. Muna godiya ainun.

      Reply
    • Bashir Yahuza Malumfashi says:
      3 years ago

      Amin, Bahaɗejen.

      Reply

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Katsina State at 37: Reflecting on Successes, Challenges, and the Way Forward

Katsina State at 37: Reflecting on Successes, Challenges, and the Way Forward

September 23, 2024
TSOKACINMU NA YAU (09)

TSOKACINMU NA YAU (09)

March 9, 2025
A Mako Ɗaya Kacal: Jami’an NDLEA Sun Yi Wawan Kamun Muggan Ƙwayoyi A Abuja, Lagos Da Sassan Nigeria

A Mako Ɗaya Kacal: Jami’an NDLEA Sun Yi Wawan Kamun Muggan Ƙwayoyi A Abuja, Lagos Da Sassan Nigeria

July 17, 2023
RAMADAN KARIM: 10-1447

RAMADAN KARIM: 10-1447

February 27, 2026

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Injiniya Tukur Hassan Tingilin (1978-2026)
  • RAMADAN KARIM: 16-1447
  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (7)

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

RAMADAN KARIM: 16-1447

Injiniya Tukur Hassan Tingilin (1978-2026)

March 5, 2026
RAMADAN KARIM: 16-1447

RAMADAN KARIM: 16-1447

March 5, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.