Rigakafi Ne Babban Jagoran Yaƙi Da Sankarar Mahaifa – Janar Buratai
Daga Bashir Yahuza Malumfashi
Jakadan Najeriya a Jamhuriyar Benin, Laftanar-Janar Tukur Yusuf Buratai (mai ritaya), CFR, ya ja hankalin al’umma, musamman mata da su maida hankali wajen kula da lafiyarsu ta hanyar kula da matakan rigakafi, domin yaƙi da cutar Sankarar Mahaifa da ta Yoyon Fitsari da ke barazana gare su a yayin ɗaukar ciki ko wajen haihuwa.
Buratai, wanda shi ne Garkuwan Keffi kuma Betaren Biu, yayi wannan jan hankali ne a yayin gabatar da jawabi, a matsayinsa na Babban Baƙo na Musamman, a Bikin Ƙaddamar da littafin wasan kwaikwayo mai suna NADAMA, wanda ya gudana a zauren taron Aso na International Conference Centre, Abuja a ranar Asabar (6-4-2023).
Tun da farko, ya gode wa marubuciyar littafin, Malama Fatima Sanda Usara, da ta gayyace shi a matsayin Babban Baƙo na Musamman. Haka kuma ya yaba mata saboda namijin ƙoƙarin da ta yi na rubuta littafin, wanda ya ce zai taimaka matuƙa wajen faɗakar da mata, domin daƙile wannan cuta da ke sanadiyyar halaka mata da dama a ƙasar nan.
Ya kuma gode wa Shugaban Kwamitin Ƙaddamarwa, Farfesa Umar Adam Katsayal, wanda kuma ya kasance mai sharhi kan littafin. Ya taya shi murna, kasancewar Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya naɗa shi muƙamin Shugaban Jami’ar Sufuri ta Gwamnatin Tarayya da ke Daura na farko.
Da yake karin bayani game da haɗari da ƙalubalen da ke tattare da cutar Sankarar Mahaifa, Janar Buratai ya ce a wani nazari da ya gudanar, ya karanta nazarin Farfesa Oliver Ezechi, Daraktan Bincike na Cibiyar Binciken Cututtuka ta Najeriya (NIMR), wanda ya bayyana cewa: “Akwai ƙiyasin cewa mata a Najeriya kimanin miliyan 36 da ke tsakanin shekara 15 zuwa sama, suna fuskantar barazanar kamuwa da cutar Sankarar Mahaifa. Haka kuma a kowace shekara ana magance majinyata dubu 12, ake kuma samun mutuwar mata dubu 8. Hakan ke nuna cewa a kullum ana samun masu kamuwa da cutar adadin 33, inda mata 22 ke rasa ransu a kowace rana a Najeriya.”
A kan haka Buratai ya buƙaci hukumomi, majalisu da dukkan masu ruwa da tsaki a harkar lafiya da ɗaukacin al’umma da su maida hankali wajen rigakafi domin a taru a kashe mahaukacin kare, ma’ana, a magance cutar Sankarar Mahaifa da Yoyon Fitsari da ke barazana ga dubban mata a Najeriya.
Da ya juya kan littafin NADAMA kuwa, ya ce saboda muhimmancinsa, yana shawartar al’umma da su mallaki littafin, domin fa’idantuwa da ilimin da ke cikinsa.
“Yana koyar da tsarin kiwon lafiya, kamar yadda yake gargaɗi game da munanan laifukan da ke faruwa a cikin al’umma, musamman masu cutar da mata,” in ji Buratai.
Haka kuma ya buƙaci da a fassara littafin zuwa yarukan Ingilishi da Yarabanci da Ibo, domin saƙonsa ya mamaye ko’ina. A kan haka ya yi alƙawarin zai tallafa da kuɗi, domin ganin an samar da na Ingilishin, sannan ya buƙaci ɗaya daga manyan mata da suka halarci taron, Uwargidan tsohon Gwamnan Jihar Imo, Zinariya Neoma Nkechi Rochas Okorocha da ta bayar da tallafi wajen ganin an fassara littafin zuwa harshen Ibo.
Bikin dai ya samu halartar muhimman mutane daga sassa daban-daban na ƙasar nan, waɗanda suka haɗa da Alhaji Zikrullah Kunle Hassan, Shugaban Hukumar Al’amuran Hajji ta Najeriya da Farfesa Ahmed Ahidjo, Shugaban Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri da Farfesa Umar Adam Katsayal, Shugaban Jami’ar Sufuri ta Tarayya Daura da Farfesa Ibrahim Malumfashi na Jami’ar Jihar Kaduna da wakilan hukumomin Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya da na Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa da sauran al’umma, maza da mata.














Masha Allah
Alhamdu lillah!
Saura Sharhi kan Littafin NADAMA, da na hango an kaddamar da shi a Abuja kwanakin baya
In sha Allah!