Fasihin Galadiman Katsina, Bashir Yahuza Malumfashi ya taya Alhaji Shehu Musa Ɗankano murnar cika shekara biyar da naɗin sa Sarautar Ɗan’iyan Galadiman Katsina.
Shi dai Ɗan’iya, a shekarar 2018 ce marigayi Galadiman Katsina na 10, Mai Shari’a Mamman Nasir ne ya naɗa shi, inda ya zama ɗaya daga cikin fadawa mafi kusa da Galadima.
A lokacin da aka tabbatar masa da sarautar, ‘yan uwa da abokan arziƙi sun fitar da takardar taya murna, inda a ciki suke cewa: “Muna murna da wannan muhimmiyar sarauta da aka ba ɗan uwanmu Alhaji Shehu Musa Ɗankano, mutum mai kishi, mai taimakon al’umma, wanda halattacen ɗan Malumfashi ne, Garin Galadima.
“Galadiman Katsina, Mai Shari’a Mamman Nasir, GCON ne ya tabbatar masa da sarautar, bayan kula ta musamman da kyawawan halayensa da asalinsa.”
A yayin da yake taya shi murna, Fasihin Galadima ya bayyana cewa Sarautar Ɗan’iya babbar sarauta ce, domin kuwa yana ɗaya daga na hannun daman Galadima, mai ba shi shawara ta musamman game da al’amuran da suka shafi dukkan masarautar Galadiman Katsina.
“An naɗa Shehu Musa a ranar Lahadi, 13-05-2018, a Fadar Galadiman Katsina da ke Malumfashi da misalin ƙarfe 10 na safe.
“A madadin ni kaina Fasihin Galadiman Katsina da iyalina, muna taya Ɗan’iya Alhaji Shehu Musa murnar cika shekara biyar a sarauta, tare da addu’ar Allah Ya ƙara jagora da lafiya, a gare ka da iyalinka, in ji Bashir Yahuza.














Ma sha Allah
Alhamdu lillah.