Daga Shanshani
Ni fa na yi zaton tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Abubakar Badaru ɗan Izala ne, musamman yadda na ga dukkan al’amuransa na addini tare da shugabannin Ƙungiyar Izala yake yi, su Sheikh Abdullahi Bala Lau da Sakatarensa, Sheikh Muhammad Kabir Gombe.
To, idan shi ɗan Izala ne, me ya sanya ya yi wa Shugaban Ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ruku’u, a yayin da yake gaisawa da shi? Ni a zatona, da shi ɗan Izala ne na gaske, tsayuwar Kabbarar Harama zai yi ƙiƙam, ya miƙa masa hannu!
To, idan shi ba ɗan Izala ba ne, to yaushe ya shiga Tijjaniyya? Kuma me yake nema a hannun Tinubu da yake wannan ranƙwafe-ranƙwafe? Shin ba kwanan nan ya gama mulkin Jihar Jigawa na tsawon shekaru takwas ba?
To, ai shi ke nan! Ke yarinya mai shago, miƙo mani robar soɓo mai sanyi, in taɓa!













