Daga Bashir Yahuza Malumfashi
Sabon Manajan Daraktan Hukumar Ruwa ta Jihar Katsina, Injiniya Tukur Hassan Tingilin ya bayyana cewa zai yi iya ƙoƙarinsa wajen zamanantar da ayyukan hukumar, domin ta dace da zamani da zimmar samar da wadatacce kuma ingantaccen ruwan sha da sauran buƙatu a faɗin Jihar Katsina.
Injiniya Tukur, wanda a makon nan ne Gwamna Malam Dikko Raɗɗa ya tabbatar masa da muƙamin na Manajan Darakta, ya shaida wa Taskar Gizago cewa zai faɗaɗa ayyukan hukumar ta haɗa hannu da ƙwararru a sassan duniya domin samar da gamsasshen aiki ga al’umma dangane da abin da ya shafi ruwa.
“Za mu jawo hukumomi da ƙungiyoyin ba da tallafi na duniya ta fuskar ruwa kuma za mu haɗa hannu da ƙwararrun kamfanoni na ƙasashen da suka ci gaba, domin kawo wa jiharmu gagarumin ci gaba ta fuskar ruwa, da yardar Allah,” in ji Injiniya Tukur.
Shi dai Injiniya Tukur Tingilin, an haife shi a garin Malumfashi, Jihar Katsina a ranar 10 ga Yuni, 1987. Ya yi karatu a fannin Injiniya ƙarafa a makarantu daban-daban, inda kuma ya ƙarƙare da Digirin-Digirgir (phD) a Jami’ar Beijing, China.













