Barkanmu Da Shiga Watan Dhul-Hijjah 1447

__________
A yau mun shiga kwanaki masu albarka na watan Dhul-Hijjah 1447 (Hijiriyya), kwanaki goma waɗanda Allah Maɗaukakin Sarki ya fifita a kan sauran kwanakin duniya saboda girman ibada da lada da suke tattare da su.
Wannan wata dama ce ga kowane Musulmi, domin ya kusanci Ubangijinsa ta hanyar ibada, tuba, kyautatawa da yawaita ayyukan alheri.
Allah ya rantse da waɗannan kwanaki a cikin Alƙur’ani mai girma. Wannan yake nuna girman matsayinsu. Allah Maɗaukakin Sarki ya ce: “Ina rantsuwa da alfijir da kuma kwanaki goma.” (Suratul Fajr-89:1-2). Malamai da dama sun bayyana cewa waɗannan kwanaki goma su ne kwanakin farko na Dhul Hijjah.
Manzon Allah (saw) ya bayyana falalar waɗannan kwanaki, a cikin wani hadisi mashahuri da Imam Bukhari ya ruwaito, inda ya ce: “Babu wasu kwanaki da aikin ƙwarai ya fi soyuwa ga Allah a cikinsu sama da waɗannan kwanaki goma.” Sahabbai suka tambaya: “Ko da jihadi a tafarkin Allah?” Sai ya ce: “Ko da jihadi, sai dai mutumin da ya fita da ransa da dukiyarsa bai dawo da komai ba.”
Wannan hadisi yana nuna cewa ibada a waɗannan kwanaki tana da matsayi mai girma ƙwarai a wajen Allah.
Daga cikin abubuwan da ake so Musulmi su yawaita yi, akwai sallar nafila, azumi, karatun Alƙur’ani, zikiri, istigfari da sada zumunta. Haka kuma, musamman akwai azumin ranar Arafah ga wanda ba ya aikin Hajji, domin Manzon Allah (saw) ya ce yana kankare zunuban shekarar da ta gabata da kuma mai zuwa.
Haka kuma ana son a yawaita faɗin: Allahu Akbar, Allahu Akbar, La ilaha illallahu Wallahu Akbar, Allahu Akbar Walillahil Hamd. Wannan zikiri yana daga cikin manyan ayyukan da ake raya waɗannan kwanaki da su.
Waɗannan kwanaki kuma lokaci ne na tuba ta gaskiya. Mutum ya duba rayuwarsa, ya nemi gafarar Allah daga kurakuransa, ya nisanci zalunci, hassada, gulma da duk wani saɓon da zai iya hana rahamar Allah sauka a gare shi. Allah Maɗaukakin Sarki Ya ce: “Ku tuba zuwa ga Allah gaba ɗaya, ya ku muminai, domin ku sami rabauta.” (Suratun Nur – 24:31). Tuba a irin waɗannan kwanaki tana da girman lada da karɓuwa idan aka yi ta da ikhlasi.
Haka kuma ana ƙarfafa kyautatawa ga iyaye, taimakon marasa ƙarfi, ciyar da mabuƙata da sadaka. Musulunci addini ne na rahama da tausayi kuma Allah yana son bayinsa masu taimakon juna. Duk wanda ya taimaki wani cikin waɗannan kwanaki, yana iya samun lada mai yawa fiye da yadda yake zato. Bai kamata Musulmi ya taƙaita ibadarsa ga kansa kawai ba. Ya kamata ya zama mai amfani ga al’umma.
Ga masu niyyar yin layya, Manzon Allah (saw) ya yi umarni cewa, idan an ga jinjirin Dhul-Hijjah, kada mutum ya rage gashi ko farce har sai ya yi layyarsa. Wannan yana daga cikin sunnonin da suke nuna girmama wannan ibada mai albarka. Layya tana tunatar da Musulmi sadaukarwar Annabi Ibrahim (AS) da biyayyarsa ga umarnin Allah. Saboda haka, ya dace Musulmi ya yi layya cikin tsoron Allah da kyakkyawar niyya.
Babu shakka, kwanaki goma na Dhul-Hijjah wata babbar dama ce da ba kowa yake riskarta ba. Masu hikima su ne waɗanda suke anfani da ita wajen tara ayyukan alheri kafin rayuwa ta ƙare. Mu yawaita addu’a, domin Allah ya gafarta mana zunubanmu, ya gyara al’amuranmu, ya kawo zaman lafiya da albarka a ƙasarmu da al’ummarmu.
Allah ya sa mu kasance cikin bayinsa nagari, masu anfani da waɗannan kwanaki masu albarka. Amin-Summa-Amin.
__________













