Yadda Babban Jigon Jam’iyyar APC Daga Kano Ya Mutu A Otel
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

__________
An samu cikakken rahoton da ke tabbatar da yadda Mataimakin Sakataren Tsare-Tsare na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano, Abdulsalami Ginsau ya rasu a otel ɗin Chida Hotels da ke yankin Utako a Abuja.
Ginsau, wanda lauya ne, shi ne shugaban kwamitin da aka ɗora wa alhakin shirya masaukai ga wakilan Jihar Kano da suka halarci babban taron APC da aka kammala kwanan nan a Abuja.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa ya rasu ne a ranar Juma’a, 27 ga Maris, bayan da ake zargin ya maƙale a cikin lalatattar lifta (elevator) a cikin otel ɗin.
Da yake magana kan lamarin, Shugaban Jam’iyyar APC na Jihar Kano, Umar Haruna Doguwa ya ce Ginsau, a matsayinsa na wanda aka ɗora wa alhakin samar da masaukai ga wakilai, ya isa Abuja tun kwana guda kafin taron, domin ya kama ɗakuna ga mahalarta taron daga jihar.
Ya ce bayan ya kammala shirya wa wakilan masaukai, Ginsau ya sauka a otel ɗin Chida Hotels. Doguwa ya ce sun fara zargin akwai matsala, lokacin da ba su ga Ginsau ba a yayin taron a ranar Juma’a, wanda ya sa suka fara nemansa, domin sanin inda ya maƙale.
Ya ce a yayin binciken da suka yi a ko’ina cikin Abuja, sun je ofishin ‘yan sanda na Utako domin kai rahoto, inda aka sanar da su cewa an samu wani lamari a otel ɗin Chida, wanda aka kawo masu rahoto.
Doguwa ya ce da suka isa otel ɗin, sun gano gawar marigayi Ginsau, inda ya ɗora laifin rasuwarsa ga sakacin hukumar gudanarwa ta otel ɗin.
A cewarsa, wasu wakilai da ke zaune a otel ɗin, sun taɓa nuna damuwa, cewa liftar otel ɗin tana da matsala. Ya ce an kai gawar mamacin domin a yi binciken sanadin mutuwarsa kuma suna jiran sakamakon binciken ‘yan sanda.
Wata majiyar ‘yan sanda ta bayyana cewa, mahukuntan Chida Hotels sun kai rahoton lamarin a hedikwatar ofishinsu a ranar Asabar, 28 ga Maris, kuma ana ci gaba da bincike.
“Chida Hotels sun zo sun bayar da rahoton cewa an samu wani lamari kuma muna bincikensa. Nazarin gawar da ake yi wani ɓangare ne na binciken. Ofishin yana ci gaba da bincike sosai,” in ji majiyar.
Lokacin da aka tuntuɓi manajan otel din, Princess Oluchi, ta ce ba za su yi wani bayani ba saboda ana ci gaba da binciken ‘yan sanda. Sai dai wata majiya a cikin otel ɗin ta yi ƙarin bayani kan abin da ya faru.
Dangane da abin da ya faru, wata majiya daga otel ɗin ta ce ɗaya daga cikin liftocin otel ɗin ta lalace kuma aka tilasta buɗe ta. Ta ƙara da cewa marigayin wanda ke zaune a hawa na uku, ya fito daga ɗakinsa ya shiga lifta ɗin da ta lalace da sassafe ranar Juma’a, inda a cikin wannan yanayi liftar ta nutse da shi a ciki ba tare da mahukuntan otel ɗin sun sani ba.
A wannan lokaci, duk wakilan da ke zaune a otel ɗin sun tafi wajen taron, ba tare da sanin cewa wani mummunan abu ya faru ba.
Majiyar ta ce washegari ne otel ɗin ya fara jin wari mai muni, wanda ya sa aka fara bincike, inda aka gano gawar marigayin.
Da yake magana a madadin iyalan, wani mai kula da marigayin, Hamza Haladu, ya bayyana lamarin a matsayin abin mamaki, yana mai cewa marigayin yana cikin ƙoshin lafiya kafin tafiyarsa Abuja.
“Yana cikin ƙoshin lafiya kuma cike da kuzari lokacin da ya tafi. Labarin rasuwarsa ya zo mana a matsayin babban abin mamaki,” in ji shi.
Marigayi Ginsau, fitaccen lauya kuma jigo a jam’iyya, an zaɓe shi kwanan nan a matsayin Sakataren Tsare-Tsare na Jam’iyyar APC a Jihar Kano.
Ya taɓa zama Babban Daraktan Kamfanin Ginsau & Sons kuma ya yi aikin lauya a Ginsau & Co. Advocates. An san shi da ƙwarewa a fannin dokokin kamfanoni da kasuwanci. Haka kuma ya riƙe muƙamin lauya a H.H. Karkasara & Co., inda ya ƙware a fannin kadarori, haraji da sauransu.
Ya yi karatu a Jami’ar Musulunci da ke Uganda da kuma Makarantar Lauyoyi ta Najeriya da ke Abuja, inda ya gina sana’ar da ta haɗa shugabanci a kasuwanci da kuma aikin lauya.
A cikin APC, ana kallonsa a matsayin jigo, wanda tasirinsa ya wuce harkokin Shari’a, domin yana da ƙwarewa a fannin dabarun siyasa da shugabanci. Ya rasu ya bar mata biyu da ‘ya’ya biyu.
__________













