RAMADAN KARIM: 26-1447

__________
‘Yan uwa, ina yi maku sallama irin ta Musulunci, Assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatuhu. Yau Lahadi, Allah ya nuna mana rana ta 26 a Ramadan. Yau ma ga nasiharmu:
Ma sha Allah! Tafiya dai tana ta gangarawa. Haka rayuwa take, a yau mun shiga azumi na 26. A yau nasiharmu za ta karkata ne zuwa ga harshenmu. Ma’ana, mu zamo masu taka-tsan-tsan wajen irin kalaman da za mu riƙa furtawa. Mu kiyayi maganganu marasa amfani ko zantukan tozarta wani ko giba ko annamimanci. Mu kiyayi kalamai yasassu. A kodayaushe idan mun tashi magana, to mu faɗi alheri ko kuma mu kama bakunanmu.
Allah (swt) a cikin Suratul Isra’i 17:53, ya ce: “Su faɗi abin da ya fi kyau.” Manzon Allah (saw) a Hadisin Imam Tirmizi mai lamba 2501, ya ce: “Wanda ya yi shiru ya tsira.”
Ya Allah, ka ba mu ikon mallakar harsunanmu, domin mu riƙa faɗin alheri kawai. Allah ka sanya mu cikin ‘yantattu a wannan wata da bayansa, Amin.
__________












