• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Monday, April 6, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Adabi

FITILAR MATASA – Zannan Galadima (2)

FITILAR MATASA

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
March 1, 2026
in Adabi
0
FITILAR MATASA – Zannan Galadima (2)

Fitilar Matasa (02)

24
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

FITILAR MATASA – Zannan Galadima (2)

Fitilar Matasa (02)

__________

Related posts

FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

March 7, 2026
Let’s Speak Our Mother Tongue

Mu Yi Kishi Da Alfahari Da Harshen Uwa

March 6, 2026

BABI NA BIYU

√ Wane Ne Tukur Tingilin?

Masu iya magana sun ce, a san mutum a san cinikinsa, ko kasuwa a san dillali. Shin wane ne Tukur? Yaushe kuma a ina aka haife shi? Su wane ne iyayensa, kuma yaya rayuwarsa ta kasance, tun daga yarinta har zuwa yau da muke rubuta wannan babi?

Kamar yadda ake ta jin Tukur…Tukur…Tukur, to cikakken sunansa dai Tukur Hassan Tingilin. An haife shi a Unguwar Tingilin Malumfashi, Ƙaramar Hukumar Malumfashi, Jihar Katsina, a ranar Asabar – 4 ga Rajab, 1398 (Hijiriyya), daidai da 10 ga Yuni, 1978 (Miladiyya).

√ Su Wane Ne Iyayensa?

Sunan mahaifinsa Malam Hassan kuma shi ma ɗan asalin Malumfashi ne, wanda ya yi makarantar Allo a Unguwar Holi, Malumfashi, a Makarantar Malam Lawal. A nan gidan Malam ya zauna a matsayin Almajiri har zuwa adadin lokacin da ya mallaki abin da ake buƙata na ilimin Ƙur’ani. Daga bisani ne ya tashi daga Unguwar Holi, zuwa Unguwar Tingilin, inda ya gudanar da rayuwarsa ta iyali.

Malam Hassan ɗan kasuwa ne. Ya yi harkar kasuwanci a kasuwar Malumfashi, har zuwa lokacin da Allah ya amshi rayuwarsa. Ya rasu a cikin watan Janairu na shekarar 1991, bayan rashin lafiya, shekara 36 ke nan a yanzu (2026). Allah ya ji ƙan shi da rahama, amin.

Mahaifiyar Tukur, Hajiya Zainabu, ita ma ‘yar Malumfashi ce kuma ‘yar uwa ce ga mahaifinsa, domin kuwa abokiyar wasansa ce. Zumunci ne ya yi ranarsa, ya ƙarfafa, har ya kai su ga aure kuma suka rayu da juna har sai da ta Allah ta raba – mutuwa.

Hajiya Zainabu ta ci gaba da rayuwa har zuwa watan Nuwamba na shekarar 2018, shekara 8 ke nan yau da ita ma ta koma ga Allah mahalicci. Tun daga wannan lokaci, Tukur ya zama maraya gaba da baya. Kodayake an ce babu maraya sai raggo. Tabbas, Tukur ba raggo ba ne, kamar yadda za mu gani a yadda rayuwarsa ta gudana a bayansu har zuwa yau ɗin nan.

ZA MU CI GABA IN SHA ALLAH!

__________

Previous Post

Yunƙurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (14)

Next Post

RAMADAN KARIM: 13-1447

Related Posts

FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)
Adabi

FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

March 7, 2026
Let’s Speak Our Mother Tongue
Adabi

Mu Yi Kishi Da Alfahari Da Harshen Uwa

March 6, 2026
FITILAR MATASA – Zannan Galadima (2)
Adabi

FITILAR MATASA – Zannan Galadima (2)

February 25, 2026
Next Post
RAMADAN KARIM: 13-1447

RAMADAN KARIM: 13-1447

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

BAKIN JAƁA (3)

BAKIN JAƁA (3)

September 9, 2025
TSOKACINMU NA YAU (04)

TSOKACINMU NA YAU (04)

March 4, 2025
SANA’AR NOMA: Ya Dace Attajirai Su Tallafa Wa Matasan Arewa – Dokta Sharif Almuhajir

SANA’AR NOMA: Ya Dace Attajirai Su Tallafa Wa Matasan Arewa – Dokta Sharif Almuhajir

September 17, 2023
Muhammadu (Saw): Haske Mai Haskakawa

Muhammadu (Saw): Haske Mai Haskakawa

November 21, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Double or Die: Thrills, Suspense and Puzzles
  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (9)
  • JOS! JOS!! JOS: Muhimmin Saƙo Zuwa Ga Musulmi Da Kirista

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Double or Die: Thrills, Suspense and Puzzles

Double or Die: Thrills, Suspense and Puzzles

April 5, 2026
Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (9)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (9)

April 4, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.