• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Saturday, April 18, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Adabi

Dalilan Da Suka Sanya Na Rubuta Littafin Tarihin Maitatsine

ADABI

Prof. Dauda Ojobi by Prof. Dauda Ojobi
December 6, 2025
in Adabi
0
Dalilan Da Suka Sanya Na Rubuta Littafin Tarihin Maitatsine

Farfesa Dauda Ojobi, SAN da kuma littafinsa na Tarihin Muhammadu Marwa Maitatsine

119
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Dalilan Da Suka Sanya Na Rubuta Littafin Tarihin Maitatsine

Daga Farfesa Dauda Ojobi

Related posts

Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza

Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza

April 11, 2026
FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

March 7, 2026
Farfesa Dauda Ojobi, SAN da kuma littafinsa na Tarihin Muhammadu Marwa Maitatsine


                            •••••••
Shahararren malamin Musulunci, Farfesa Dauda Ojobi ya shahara wajen muƙabala dangane da addinan Musulunci da Kiristanci, kamar yadda ya yi suna wajen wallafa littattafan tarihin addinai da makamantansu, ya fitar da sabon littafinsa, wanda ya rubuta a kan tarihin Muhammadu Marwa Maitatsine.

Shin waɗanne dalilai ne suka sanya malamin ya rubuta wannan littafi? Ga wasu dalilai guda huɗu da mawallafin ya fitar dangane da wannan mashahurin littafin:

√ Maganar Wani Malami A Katsina:
Wannan shi ne abu na farko da ya fara janyo hankalina a kan in yi bincike mai zurfi dangane da Maitatsine.

A shekarar 2023 aka samu wani Malami kuma shugaban ƙungiyar masu bin koyarwar Maitatsine a Jihar Katsina, mai suna Dr. Isma’il Zakariyya Al-Kashnawy. Shi ne ya fito ƙarara ya ce: “Muhammadu Marwa Maitatsine, zaluntarsa aka yi kuma za mu rama wannan zaluncin da aka yi masa.”

Lallai wannan maganar ta girgiza hukumomi a lokacin saboda a cikin sati ɗaya sai aka ji wannan malamin ya ƙara fitowa yana cewa: ” Na ba da haƙuri a kan maganar da na yi satin da ya gabata saboda ta yi wa wasu zafi.”

Dalili na farko ke nan da ya sa na zabura, domin tattaro tarihin Maitatsine saboda in san wane ne shi kuma mene ne ya faru da shi?

√ Babu Wani Gamsasshen Rubutu A Kan Tarihin Maitatsine:
A lokacin da na zabura domin tattaro bayanai, sai na lura cewa a rubuce, gaskiya babu wani gamsasshen rubutu a kan tarihin Maitatsine, tun daga farkon rayuwarsa har zuwa mutuwarsa. A inda na tarar cewa mafi yawan littattafan sun karkata ne kawai zuwa ga wani abu ɗaya ko biyu game da maitatsine.

Daga cikin littattafan da aka yi rubuta a kan Maitatsine, akwai: 1-The Kano Disturbances Tribunal of Inquiry. 2-The New Nigerian Newspaper (1979, 1980, 1981, 1982). 3-The New Standard Newspaper (1979, 1980, 1981, 1982). 4-The Maitatsine Risings in Nigeria by Elizabeth Isichei. 5-The Maitatsine by Nasiru Zaharaddeen. 6-Hira ta musamman a kan tarihin Maitatsine, a Gidan Rediyon Rahama ta Jihar Kano. 7-‘Yan Al-Kur’aniyyun, ‘Yan Tatsine, Ƙalaƙato: Tarihin Kafuwarsu Da Aƙidunsu, Daga Sheikh Ja’afar Mahmud Adam.

Waɗannan su ne littafai da bayanai, waɗanda na samu a taƙaice game da tarihin Maitatsine.

√ Na Ƙuduri Rubuta Tarihin Maitatsine Domin Ankarar Da Al’ummar Baya:
Lallai wannan shi ne babban maƙasudina na wannan aiki. Kodayake tabbas hukumomin ƙasarmu ba su wasa da bibiyar ƙananan labarai, sai dai kash, idan sun gano matsala, to ɗaukar mataki yana zama musu wani aiki mai wahala. Ina fatan Allah ya taimake su a kan aiki da gaskiya kuma ya sauwaƙe musu bin ta, Amin.

√ Rashin Adalcin Wasu Daga Cikin Waɗanda Suka Yi Rubutu A Kan Maitatsine:
Tabbas wasu daga cikin marubuta sun ɓoye gaskiya a kan ilimi ko akasin hakan. Sannan sun canza asalin abin da ya faru, shi ma a kan ilimi ko akasin hakan. Sannan sun yi rashin adalci ga harkar almajiranci da sauran wasu al’amura da suke da alaƙa da Musulunci.
_______________

Previous Post

Yau Take Juma’a: Allah Ka Albarkace Mu

Next Post

Army Chiefs Issue Strong Warning to Sahara Reporters Over Allegations

Related Posts

Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza
Adabi

Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza

April 11, 2026
FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)
Adabi

FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

March 7, 2026
Let’s Speak Our Mother Tongue
Adabi

Mu Yi Kishi Da Alfahari Da Harshen Uwa

March 6, 2026
Next Post
Army Chiefs Issue Strong Warning to Sahara Reporters Over Allegations

Army Chiefs Issue Strong Warning to Sahara Reporters Over Allegations

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Mummunar Zanza-Zanga A Ƙasar Nepal

Mummunar Zanza-Zanga A Ƙasar Nepal

September 11, 2025
Abdullahi Garba Faskari Ne Sabon Sakataren Gwamnatin Katsina

Abdullahi Garba Faskari Ne Sabon Sakataren Gwamnatin Katsina

August 7, 2023
Lallai Hukuma Ta Tallafa Wa Marubuta Domin Yaƙar Jahilci – Sheikh Gamawa

NASIHAR JUMU’A: Daga Sheikh Aliyu Said Gamawa

September 1, 2023
Taya Ni Mu Gyara: Kisan Baƙi Sai Gayya

Taya Ni Mu Gyara: Kisan Baƙi Sai Gayya

November 1, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Ko Me Ya Sa Manyan Mata Ke Auren Yara?
  • Mu Ji Tsoron Allah
  • Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Ko Me Ya Sa Manyan Mata Ke Auren Yara?

Ko Me Ya Sa Manyan Mata Ke Auren Yara?

April 18, 2026
Mu Ji Tsoron Allah

Mu Ji Tsoron Allah

April 17, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.