• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Thursday, June 18, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Babban Labari

Hukumar NDLEA Ta Kama Ɗan Indiya Da Muggan Ƙwayoyi Na Naira Biliyan 3.9

BABBAN LABARI

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
September 17, 2025
in Babban Labari
0
Hukumar NDLEA Ta Kama Ɗan Indiya Da Muggan Ƙwayoyi Na Naira Biliyan 3.9

Gupta Ravi Kumar, ɗan Indiya da aka kama da safarar ƙwaya

5
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Hukumar NDLEA Ta Kama Ɗan Indiya Da Muggan Ƙwayoyi Na Naira Biliyan 3.9

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Sojan Gona: An Kama Sojan Bogi Mai Muƙamin Manjo-Janar

Sojan Gona: An Kama Sojan Bogi Mai Muƙamin Manjo-Janar

June 12, 2026
Kotu Ta Ayyana Hausawa Da Fulani Halastattun ‘Yan Ƙasa A Jihar Filato

Kotu Ta Ayyana Hausawa Da Fulani Halastattun ‘Yan Ƙasa A Jihar Filato

June 11, 2026
Shi ma jami’an NDLEA suka kama shi

 

__________
Wani ɗan kasuwa ɗan Indiya, Gupta Ravi Kumar, tare da wasu ‘yan Najeriya uku: Ogunlana Noah Olanrewaju, Olushola Idrees Kayode da Bakare Korede Muheeb sun shiga hannun jami’an hukumar NDLEA, sakamakon kama su da aka yi da kwalabe miliyan biyu da dubu 248 na Tramadol (200mg/225mg) a Filin Jirgin Sama na Murtala Muhammed (MMIA), Ikeja, Lagos.

Wannan Tramadol da aka kama, kamar yadda Daraktan Watsa Labarai na Hukumar, Femi Babafemi ya bayyana, ya kai darajarta Naira biliyan 3.9 kuma an shigo da shi ne daga Delhi, Babban Birnin ƙasar Indiya. An samu maganin ne a ɓoye cikin katon-katon 114. Jami’an hukumar sun bankaɗo shi ne a wani jirgin Ethiopian Airlines da ya iso Legas a ranar Litinin, 8 ga Satumba, 2025.

Su ma sun shiga hannun NDLEA

“Yadda lamarin ya faru shi ne, bayan isowar jirgin daga Indiya, jami’anmu sun saka ido a kansa, inda cikin lokaci suka yi dirar mikiya kan wani dillalin shigo da kaya da direbobi biyu, waɗanda suka yi ƙoƙarin fitar da kayan da manyan motoci biyu ranar Juma’a, 11 ga Satumba.” A cewar Jami’in Watsa Labaran Hukumar, Femi. Ya ƙara da cewa, wannan bincike ne ya kai su ga kama ɗan kasuwar mai suna Gupta Ravi Kumar, yayin da yake ƙoƙarin karɓar kayan.

Haka kuma, a wani ƙoƙarin, jami’an na NDLEA, a ranar Lahadi, 7 ga Satumba, sun kama wani fasinja, Onyeganochi Stanley Ifeanyi, da yake kan hanyarsa ta zuwa birnin Doha a jirgin Qatar Airlines. Da suka bincika akwatinsa, sun gano tabar wiwi mai nauyin giram 900. Ya ce wani ɗan Najeriya ne da ke zaune a Qatar, Ohadiegwu Anthony Uchenna, ya ba shi akwatin don ya kai masa Doha.

Da jami’an suka tsananta bincike, sun sake cafke Uchenna, wanda ya raka shi filin jirgin. A ɗakinsa da ke Ajao Estate, an gano ƙarin giram 200 na wannan tabar. Ya amsa cewa shi ne zai dawo daga Doha daga baya ya karɓi akwatin idan Onyeganochi ya tsallake binciken tsaro.

Su ma sun shiga hannu

Shugaban Hukumar NDLEA, Birgediya Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya) ya yaba da ƙoƙarin jami’an nasa da ke aiki a sassa daban-daban na ƙasar nan. Ya kuma buƙace su da su ci gaba da bin tsarin daidaito wajen yaƙi da miyagun ƙwayoyi.
__________

Previous Post

BAKIN JAƁA (4)

Next Post

Abin Da Ya Sa Na Naɗa Mataimaka 85 – Ciyaman Mukhtari City

Related Posts

Sojan Gona: An Kama Sojan Bogi Mai Muƙamin Manjo-Janar
Babban Labari

Sojan Gona: An Kama Sojan Bogi Mai Muƙamin Manjo-Janar

June 12, 2026
Kotu Ta Ayyana Hausawa Da Fulani Halastattun ‘Yan Ƙasa A Jihar Filato
Babban Labari

Kotu Ta Ayyana Hausawa Da Fulani Halastattun ‘Yan Ƙasa A Jihar Filato

June 11, 2026
Ta Banka Wa Mijinta, Kishiyarta Da Yara Wuta A Kano
Babban Labari

Ta Banka Wa Mijinta, Kishiyarta Da Yara Wuta A Kano

May 13, 2026
Next Post
Abin Da Ya Sa Na Naɗa Mataimaka 85 – Ciyaman Mukhtari City

Abin Da Ya Sa Na Naɗa Mataimaka 85 - Ciyaman Mukhtari City

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

TURBANIN CEREMONY OF SARKIN GABAS OF TUMBU:

October 10, 2024
SANA’AR NOMA: Ya Dace Attajirai Su Tallafa Wa Matasan Arewa – Dokta Sharif Almuhajir

SANA’AR NOMA: Ya Dace Attajirai Su Tallafa Wa Matasan Arewa – Dokta Sharif Almuhajir

September 17, 2023
Ɓarawo Ya Sakar Masa Mata

Ɓarawo Ya Sakar Masa Mata

June 7, 2023
Batun Jami’a A Malumfashi: Ƙarin Bayani Daga Abdullahi Ibrahim Mahuta

Batun Jami’a A Malumfashi: Ƙarin Bayani Daga Abdullahi Ibrahim Mahuta

July 8, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Jaafar Jaafar Ya Buɗe Idanun ‘Yan Kwankwasiyya
  • Taɓarɓarewar Tsaro A Najeriya: Janar Buratai Ya Buƙaci A Ɗauki Matakan Gaugawa
  • BARKA DA SABUWAR SHEKARAR MUSULUNCI 1448 HIJIRIYYA

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Jaafar Jaafar Ya Buɗe Idanun ‘Yan Kwankwasiyya

Jaafar Jaafar Ya Buɗe Idanun ‘Yan Kwankwasiyya

June 17, 2026
Taɓarɓarewar Tsaro A Najeriya: Janar Buratai Ya Buƙaci A Ɗauki Matakan Gaugawa

Taɓarɓarewar Tsaro A Najeriya: Janar Buratai Ya Buƙaci A Ɗauki Matakan Gaugawa

June 16, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.