Sharhin Littafi:
Wasu Muhimman Darussa Daga Zantuttukan Bukar Usman
~~~~~~~
Sunan Littafi: Conversations With Bukar Usman.
Sunan Edita: Khalid Imam
Yawan Shafukan: 928
Shekarar Wallafa: 2022
Kamfanin Wallafa: Whetstone Publishers, Kano-Nigeria.
Lambar ISBN: 978-978-56734-9-5 HB
Mai Sharhi: Bashir Yahuza Malumfashi
~~~~~~~
Wannan mashahurin littafi mai take Conversations With Bukar Usman (Tattaunawa Da Bukar Usman), kundi ne da ya tattara ƙunshiyar falsafa, ilimi, kimiyyar aikin gwamnati, salailan rayuwar siyasa, hikimomi da dubarun mulki, faɗi-tashin rayuwar yau da kullum, aikin jarida, zamantakewar iyali da ma tarihin rayuwar al’umma da ta shafi mashahurin mutum, wanda a yau ya zarta shekara 80 a duniya, wanda kuma rayuwarsa ta ga jiya da yau kuma take hasko gobe – Dokta Bukar Usman, D.Litt, M.IoD, OON.
Kamar yadda sunansa ya nuna, littafin yana ƙunshe ne da jerin tattaunawa iri daban-daban daban da aka gudanar tsakanin ‘yan jarida da masana daban-daban, ya Allah a kafafen watsa labarai da suka haɗa da jaridu, mujallu, talabijin ko rediyo da ma sauran kafafen yaɗa ilimi da suka haɗa da littattafai da intanet da sauransu.
Waɗannan tattaunawa sun wakana ne na tsawon shekaru sama da 20 kuma sun samu ne ya Allah a lokacin da Dokta Bukar ke kan aikin gwamnati, ma’ana suka shafi aikinsa, zuwa bayan ya yi ritaya, a matsayinsa na marubuci, suka danganci littattafansa, ko kuma a matsayinsa na Madugun tallafa wa gajiyayyu da raunana, ta hanyar gidauniyarsa ta Bukar Usman Foundation da sauransu.
A wannan sharhi, za mu yi kurme ne cikin ƙunshiyar littafin, domin fito da wasu ƙwararan darussa na gani na faɗa, waɗanda za su kasance abin koyi ga al’ummar yau da ke raye da ma waɗanda ke tafe nan gaba ta kusa da ta nesa.
Shin wane ne Bukar Usman? Tun daga tarihinsa, wanda ya bayyana a shafukan farko da na ƙarshe, a littafin nan, mutum zai ɗauki muhimman darussa. An haifi Bukar a ranar 10 ga watan Disamba na shekarar 1942 a garin Biu, Jihar Borno da ke Arewa Maso Gabashin Nigeria. Daga 1951 zuwa 1954 ya yi karatun ƙaramar firamare a garin Biu. Daga 1955 zuwa 1963 ya yi zaman ɗalibta a Maiduguri, inda ya yi karatun sakandare. Daga nan kuma ya samu gurbin karatu a kwalejin King’s College da ke Lagos, inda ya samu ilimin gaba da sakandare. Ya yi karatun digiri a fannin Hikimar Mulkin Al’umma a Jami’ar Ahmadu Bello Zaria a shekarar 1969. Ya fara aikin gwamnati ne a matsayin Ƙaramin Ma’aikacin Ofis, a Gwamnatin Tarayyar Nigeria a shekarar 1965, inda cikin jajircewa da haƙuri da juriya, ya yi ta samun ƙarin girma, har ya kai ƙololuwar muƙamin aikin, wato Babban-Sakatare a Fadar Shugaban Ƙasa. Ya yi ritaya daga aikin gwamnati a shekarar 1999, bayan gudanar da aikin shekara 34. Daga nan ya duƙufa cikin harkokin rubutu da nazari da kuma tallafa wa mabuƙata ta hanyar gidauniyarsa. Ya samu kyaututtukan Karramawa iri-iri daga ciki da wajen Nigeria.
Daga tarihin nan kaɗai, mai karanta littafin nan zai ɗauki darussan rayuwa da suka danganci muhimmancin neman ilimi da amfaninsa. Ta hanyar ilimi ne Dokta Bukar ya zama abin da ya zama, ya samu nasara a rayuwa, ya zama mai amfani ga kansa da iyalansa da al’umma baki ɗaya. Haka kuma mutum zai koyi darasin haƙuri da juriya, waɗanda su suka kai Bukar ga nasara a fagagen duk da ya sanya gaba.
A shafi na 17 zuwa na 18, mai karatu zai ƙaru kuma ya fahimta da darasin muhimmancin taimakon al’umma, musamman idan ya yi la’akari da manufofi da dalilan da suka sanya Dokta Bukar Usman ya kafa gidauniya mai zaman kanta, gidauniyar da ta samu rijista da Hukumar Yi Wa Kamfanoni Da Ƙungiyoyi Rijista (CAC) a shekarar 2008 kuma take aikin tallafa wa al’umma tun daga lokacin har zuwa yau, babu fashi.
Daga shafi na 19 zuwa na 20, mai karatu zai fahimta da cewa littafin nan abin buƙata ne ga mai son sanin tarihin Nigeria na haƙiƙa, kamar yadda masani, Ambasada, Farfesa George A. Obiozor ya faɗa, a gabatarwar da ya rubuta.
“Wannan ɗa na Biu, shi kuma muhimmin ɗan Nigeria ne. Kuma wannan littafi, Conversations With Bukar Usman, lallai abin buƙata ne ga waɗanda ke buƙatar sanin tarihin gaskiya na Nigeria cikin sauri, tarihin faɗi-tashi da nasarorinta cikin zamunna.”
Ga ɗaliban sanin makamar aikin jarida ko ma ga duk mai son ƙarin ilimi game da aikin jarida, zai samu babban ilimi da darussa masu muhimmanci a littafin nan, musamman idan ya nazarci muƙalar da ƙwararren ɗan jarida kuma marubuci, Duve Nakolisa ya rubuta a gabatarwarsa ga littafin nan, a shafi na 21 zuwa na 31. Mutum zai ƙaru da hikimomi da dabarun tsara tambayoyi a ilimin aikin jarida. A tsokacinsa game da littafin nan, ya gano cewa, Dokta Bukar Usman ya tattauna da ‘yan jarida iri-iri, inda ya amsa tambayoyi mabambanta guda 488 daga shekarar 1996 zuwa 2021 a maudu’ai daban-daban.
Akwai darussan da suka shafi tarihi da ilimin aikin gwamnati da tsarin gudanar da mulki ga wanda ya nazarci shafi na 35 zuwa 47, watau tattaunawar Bukar Usman da ɗan jarida Shittu Obassa, wadda aka wallafa a Jaridar New Nigerian Weekly, ta ranar 3 ga Satumba, 2003.
Ga marubuci ko mai son zama marubuci mai nasara, akwai muhimman darussan da zai koya kuma ya amfana da su, idan ya karanta tattaunawar ɗan jarida Isa Sanusi da Bukar Usman a shafi na 49 zuwa 52. Tattaunawar ta fito ne a cikin Jaridar Sunday Trust ta 29 ga Oktoba, 2009. A wannan tattaunawa, ya yi bayani dalla-dalla na hanyoyi da matakan da mutum zai bi ya zama marubuci mai nasara.
Wasu darussa masu muhimmanci da suka fito a littafin nan, shafi na 53 zuwa na 58, su ne da suka shafi ‘yancin ɗan Adam. Akwai cikakken bayani na ƙwarewa daga tattaunawar ɗan jarida Samuel O. Dauda da Bukar Usman, wacce aka wallafa a Jaridar Leadership ta ranar 25 ga Disamba, 2006.
Wata tambaya mai muhimmanci da a kullum ake damun Dokta Bukar Usman da ita, ita ce, wane dalili ya sanya yake rubutu da Hausa kuma yake hidima sosai ga wannan harshe, duk da cewa shi ba Bahaushe ba, shi ɗan ƙabilar Babur ne? Ga mai irin wannan tambayar, zai samu gamsassun amsoshi a shafi na 59 zuwa na 65, a tattaunawar ɗan jarida Ashafa Murnai Barkiya, wacce aka wallafa a jaridar Leadership Hausa ta ranar 9 zuwa 15 ga Janairu, 2009. Haka kuma akwai irin waɗannan amsoshin a shafi na 67 zuwa na 73, a wata tattaunawa da ɗan jarida Bashir Yahuza Malumfashi ya yi da Bukar, wacce aka wallafa a jaridar Aminiya ta ranar 17 ga Afirilu, 2009.
Daga shafi na 75 zuwa na 86, ‘yan siyasa ko waɗanda suka samu kansu a da’irar mulki, za su koyi darussa masu muhimmanci da amfani dangane da dabaru da hikimomin da ake bi ana magance rikice-rikice da tashin hankali da kan taso a tsakanin ƙungiyoyin ƙwadago da gwamnati. Dokta Bukar Usman ya warware zare da abawa a tattaunawarsa da ɗan jarida Shittu Obassa kuma aka buga a jaridar New Nigerian Weekly, ta ranar 5 ga Disamba, 2009.
Akwai wasu darussan kuma ga ɗaliban siyasa a shafi na 87 zuwa na 92 na littafin nan, a tattaunawar Bukar da jaridar New Nigerian ta ranar 27 ga Disamba, 2009, inda ya yi fashin baƙi game da halayen shugabannin Nigeria na da da kuma na yanzu, da yadda halayen nasu ke canjawa.
An daɗe ana shirya gasa ga marubuta a Nigeria. Shin mene amfanin irin waɗannan gasa ga al’umma da su kansu marubuta? A wata tattaunawa da Bashir Yahuza Malumfashi ya yi da Dokta Bukar, aka wallafa a jaridar Aminiya ta ranar 16 ga Afirilu, 2010, an bayar da haske sosai a shafi na 93 zuwa na 97 na littafin nan.
An shiga wani zamani, inda harkar karatu da rubutu suka koma intanet, maimakon allo da takarda da alkalami. Shin ko intanet za ta murƙushe tsarin ilimi na dauri? Mai neman ƙarin bayani da gamsassar amsa, zai samu a shafi na 99 zuwa na 102 na littafin nan, a tattaunawar da jaridar Nigerian Pilot ta ranar 11 ga Afirilu, 2013 ta yi da Bukar.
Shin wane tudu, wane gangare Bukar Usman ya biyo har ya zama shahararren marubuci? An samu lokacin da a cikin shekaru bakwai kacal ya rubuta mashahuran littattafai 20. Matasan marubuta za su iya koyon darussan ƙwazo da jimiri da haƙuri daga tattaunawar Bukar Usman da ɗan jarida Abubakar Adam Ibrahim, wacce aka buga a jaridar Sunday Trust ta ranar 25 ga Agusta, 2013 kuma ta bayyana a shafi na 103 zuwa na 110 na littafin nan.
Kamar yadda aka bayyana a baya, littafin nan na Conversations With Bukar Usman kandami ne da ke ƙunshe da darussan rayuwa iri-iri. Daga shafi na 111 zuwa 116, akwai wasu muhimman tattaunawa da Bashir Yahuza Malumfashi ya yi da Bukar, aka wallafa a jaridar Weekly Trust, ta ranar 1 ga Maris, 2014 da kuma ta ranar 12 ga Afirilu, 2014. Cikinsu, mai karatu zai ga darussan da ke nuna dalilan da kan kai mutum ga nasara da ɗaukaka a gida da wajen ƙasarsa, kamar dai yadda ta faru ga Dokta Bukar Usman, yadda aka karrama shi a Nijar a sanadiyyar hidimarsa ga adabin gargajiya. Haka ma tattaunawar Khalid Imam da shi Bukar ta nuna, a shafi na 173 zuwa na 191, wacce aka wallafa a Mujallar ANA Review, Special Anniversary Edition.
Shin wane irin salon mulki ko shugabanci ne ke samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali ga al’ummar ƙasa? A shafi na 117 zuwa na 119 na littafin nan ya ɗauko tattaunawar Dokta Bukar da Gidan Talabijin na NTA, ta watan Agusta na 2017, Yemi Adebisi na jaridar Daily Independent ya rubuta, aka wallafa a jaridar ta ranar 4 ga Satumba, 2017. Dokta ya yi bayani dalla-dalla dangane da batun. Haka ma akwai irin waɗannan darussan a shafi na 195 zuwa na 209 na littafin, a tattaunawar Dokta da Yusuf Tatu na FRCN Kaduna, a watan Maris, 1996.
Akwai darussa da ilimi da suka danganci tsarin dimokuraɗiyya da yadda farfaganda ke shafar Nigeria daga ƙasashen duniya da sauran saɓatta-juyatta da kan shafi zamantakewa tsakanin ƙasar da sauran ƙasashen duniya a shafi na 211 zuwa na 258 daga tattaunawar Bukar da Yusuf Tatu na FRCN Kaduna, ta Satumba, 1997 da kuma wadda ta gudana a watan Mayu, 1998.
Tatsuniya da almara na da matuƙar tasiri da muhimmanci wajen koya tarbiyya da nishaɗantarwa a rayuwar Malam Bahaushe. Hanyoyi ne kuma na adanawa da inganta al’adu da ɗabi’u da tarihin al’umma a ƙasar Hausa. Dokta Bukar Usman ya sanya kansa tattarawa da inganta su. A wannan tafarki, ya samu martaba da karimci a gida da wajen Nigeria. A tattaunawarsa da Ado Ahmad Gidan Dabino, a Freedom Radio Kano a 2010 da kuma tattaunawarsa da Muhammad Salisu Hamisu a Rfi Hausa a 2010, ya zayyana wasu daga muhimmancin wannan fage da dalilan da suka sanya yake masu hidima.
Duk dai a game da wannan fage na tatsuniyoyi da almara, Dokta Bukar ya tattauna da Muhamman Babalala na BBC Hausa a ranar 30 ga Yuli, 2013 da kuma Souley Mage (Regeto), a Radio Alternative FM 99.4, Yamai, Jamhuriyyar Nijar, a ranar 4 ga Fabrairu, 2014. Ya kuma tattauna da Tijjani Garga, na Gidan Rediyo da Talabijin na Jihar Borno, dangane da Ƙungiyar Nazarin Al’adun Gargajiya (NFS), a yayin taronta na 11, wanda ya gudana a Jami’ar Bayero Kano, a ranakun 2 zuwa 4 ga Afirilu, 2014. Dokta Bukar, a matsayinsa na shugaban wannan ƙungiya, ya zayyana muhimmanci da fa’idojinta da amfanin irin waɗannan taruka.
Tarihi babban al’amari ne ga kowace al’umma. Dokta Bukar ya jaddada muhimmancin da ke tattare da tarihi a yayin tattaunawarsa da Muhammad Salisu Hamisu na Rfi Hausa, a ranar 2 ga Fabrairu, 2016, aka wallafa a littafin nan, daga shafi na 367 zuwa na 369. A nan ne ya bayyana cewa, sai da ya kwashe tsawon shekara takwas yana rubuta littafin Tarihin Biu.
Wannan littafi bai bar komai ba dangane da rubuce-rubucen Dokta Bukar, domin kuwa daga shafi na 421 zuwa na 925, ƙunshe suke da rataye-rataye da suka tattaro maudu’ai daban-daban da suka danganci rubuce-rubucen yabo da ƙarfafa gwiwa, musamman ga Bukar Usman, lokacin da ya cika shekara 70 da 80 a duniya. Wani ratayen kuma ƙunshe yake da wakokin baka da rubutattu da aka yi masa. Haka kuma akwai ratayen da ke ɗauke da maƙalolin ta’aziyya da shi Bukar ya rubuta ga muhimman mutane a rayuwarsa, waɗanda suka rasu. Misalin irin fitattun mutane da suka yi wa al’umma hidima, kamar marigayi Alhaji Umaru Aliyu Shinkafi, wanda ya rasu a ranar 6 ga Yuli, 2016. Akwai maƙala a kan marigayi Shettima Ali Monguno, wanda ya rasu a ranar 8 ga Yuli, 2016. Akwai wadda ya rubuta kan Farfesa Michael Eghosa Aken’Ova, wanda ya rasu a ranar 13 ga Satumba, 2016. Akwai muƙalarsa a kan Onwa Ikenna Ndaguba, wanda ya rasu a ranar 18 ga Satumba, 2011.
Akwai rataye na musamman, wanda ke ɗauke da tarihin Bukar Usman da jaddawalin dukkan sunayen littattafan da ya rubuta da bayanin shekarun da aka wallafa su.
Wani muhimmin darasi game da rayuwar Dokta Bukar Usman, shi ne irin mu’amalarsa da irin mutanen da yake hulda da su da kuma yadda su kuma mutanen suke hulda da shi. Idan mutum ya samu shaidar kirki daga mutane, musamman waɗanda suka gamsu da tsarin rayuwarsa da ayyukansa, lallai za a iya cewa ya samu nasarar rayuwa. Akwai rataye na musamman da yake ƙunshe da tsokaci, sa albarka daga ɗimbin masana da ɗaidaikun mutane da suka yi nazari ko kuma suka karanta littattafan Bukar Usman ko maƙalolinsa ko tattaunawa a jaridu da mujallu da rediyo da talabijin.
Wasu daga cikin mashahuran mutanen da suka tofa albarkacin bakinsu game da rayuwa da ayyukan Bukar Usman sun hada da Farfesa Damian U. Opata, Dokta Suraiya Shahin, Farfesa Segun Adekoya, Farfesa AK. Babajo, Birgediya-Janar Haliru Hakilu, Dokta Tukur Ingawa, Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau, Dokta Bashir Abu Sabe, Farfesa Salisu A. Yakasai da Farfesa Alaba Ogunsanwo.
Sauran sun haɗa da Farfesa Abdullahi Y. Shehu, Farfesa Idris Amali, Farfesa Aliyu Mu’azu mni, Farfesa Aminu Ɗorayi, Dokta Abubakar Malah Umar, Dokta Safiya Isma’ila Yero, Farfesa Ibrahim Malumfashi da Farfesa Isma’ila A. Tsiga da sauransu da dama.

Babu shakka, ta dukkan yadda mutum ya kalli littafin nan na Conversations With Bukar Usman, irin yadda aka wallafa shi da inganci, ɗauke da hotuna iri-iri da wadatattun shafuka – zai same shi a matsayin babban kundin da za a iya kira da “Rumbun Ilimi, Taskar Tarihi” mai amfani ga al’umma na yanzu da kuma masu zuwa nan gaba. Littafin nan babbar haja ce da ya kamata ɗalibai da masana su mallaka, kamar kuma yadda ya kamata a tanadar da shi a ɗakunan karatu da cibiyoyin ilimi na ko’ina a ƙasar nan.













