Garin Zango Ya Samu Babban Asibiti na Farko A Tarihi
Daga Bashir Yahuza Malumfashi
__________
Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, PhD, CON, ya ƙaddamar da sabon Babban Asibiti a Zango, wanda shi ne babban asibiti na farko da aka kafa a tarihin Ƙaramar Hukumar.
An gudanar da bikin ƙaddamarwar ne a jiya Alhamis, 6 ga Agusta, 2026, inda gwamnatin jihar ta bayyana aikin a matsayin wani muhimmin mataki na inganta tsarin kiwon lafiya da kuma faɗaɗa ayyukan jinya ga al’ummar jihar.
A jawabin maraba, Kwamishinan Lafiya na Jihar Katsina, Hon. Musa Adamu Funtua, ya ce ƙaddamar da sabon asibitin wani gagarumin ci gaba ne a ƙoƙarin gwamnatin jihar na samar da ingantattun ayyukan kiwon lafiya ga jama’a. Ya bayyana cewa aikin ya nuna irin jajircewar Gwamnatin Malam Dikko Umaru Radda wajen bunƙasa harkar lafiya a faɗin jihar.
Da yake jawabi, Gwamna Radda ya gode wa Allah Maɗaukakin Sarki bisa bai wa gwamnatinsa damar kammala aikin, yana mai bayyana cewa an samar da sabon asibitin ne ta hanyar ɗaga darajar tsohuwar Cibiyar Kiwon Lafiya ta Matakin Farko da ke Zango zuwa cikakken Babban Asibiti.

Ya bayyana cewa an tanadi asibitin da sabbin kayan aikin lafiya na zamani domin gudanar da ayyukan jinya da tiyata cikin inganci. A cewarsa, hakan zai rage yawan tura marasa lafiya zuwa manyan asibitoci da ke nesa tare da sauƙaƙa samun ingantacciyar kulawar lafiya ga al’ummar Zango da maƙwabtan ƙananan hukumomi.
Gwamnan ya jaddada cewa harkar lafiya na ci gaba da kasancewa ɗaya daga cikin manyan abubuwan da gwamnatinsa ta bai wa fifiko, tun bayan hawansa mulki. Ya lissafo nasarorin da aka samu cikin shekaru uku da suka gabata, waɗanda suka haɗa da ɗaga darajar cibiyoyin kiwon lafiya guda huɗu zuwa Manyan Asibitoci, inganta wasu cibiyoyin lafiya, gyaran manyan asibitoci da ɗakunan tiyata, farfaɗo da cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko (PHCs) sama da 280, da ɗaukar sabbin ma’aikatan lafiya guda 804 aiki.
Sauran nasarorin da ya bayyana sun haɗa da gina cibiyar wankin ƙoda ta zamani (Dialysis Centre), kafa cibiyar sarrafa magunguna da kuma faɗaɗa amfani da wutar lantarki ta hasken rana a asibitocin gwamnati, domin tabbatar da ci gaba da gudanar da ayyukan lafiya.
Har ila yau, Gwamna Radda ya sanar da cewa gwamnatin jihar ta fara shirin horar da likitoci (Medical Residency Training) a fannoni shida na likitanci a manyan asibitocin jihar. Ya ƙara da cewa gwamnati na ci gaba da ɗaukar nauyin karatun ɗaliban fannin likitanci a jami’o’in cikin gida da na ƙasashen waje domin magance ƙarancin ƙwararrun ma’aikatan lafiya.
Tun da farko, Babban Manajan Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Katsina, Dr. Muhammad Nazir, ya tabbatar da cewa za a gudanar da sabon asibitin bisa ƙa’idojin ƙwarewa da inganci domin samar wa al’umma ingantattun ayyukan kiwon lafiya.
Shi ma Shugaban Jam’iyyar APC na Jihar Katsina, Dakta Bishir Gambo Saulawa, ya yaba wa gwamnatin jihar kan ci gaba da zuba jari a fannin kiwon lafiya da sauran sassan ci gaba. Ya bayyana ƙaddamar da asibitin a matsayin cika wani muhimmin alƙawarin gwamnati na inganta rayuwar al’ummar jihar.
A nasa jawabin, Shugaban Ƙaramar Hukumar Zango, Hon. Babangida Yardaje, ya gode wa Gwamna Radda bisa samar da asibitin, yana mai tabbatar masa da cewa al’ummar yankin za su ba da cikakken haɗin kai wajen kula da kayan aikin asibitin da tabbatar da dorewar ayyukansa.
A ƙarshe, Gwamna Radda ya yi kira ga al’ummar Ƙaramar Hukumar Zango da maƙwabtan yankunan, da su kare wannan katafaren asibiti tare da ba ma’aikatan lafiya cikakken haɗin kai, domin tabbatar da ingantaccen aikin kula da lafiyar jama’a.
Bikin ƙaddamar da asibitin ya samu halartar Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Katsina, Rt. Hon. Nasir Yahya Daura; Shugaban Ma’aikatan Gidan Gwamnati, Hon. Abdulkadir Mamman Nasir; Mai Ba Jam’iyyar APC Shawara ta Fuskar Shari’a, Barista Murtala Aliyu Kankia; Kwamishinan Yaɗa Labarai, Dr. Bala Salisu Zango; ‘yan takarar jam’iyyar APC; shugabannin ƙananan hukumomi; ‘yan majalisar dokoki; ‘yan siyasa da sauran masu ruwa da tsaki.
__________













