• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Friday, August 14, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Labarai

Gwamna Dikko Ya Ƙaddamar da Aikin Faɗaɗa Titin Cikin Garin Mashi Mai Tsawon Kilomita Uku

DIKKON KATSINAWA

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
August 5, 2026
in Labarai
0
Gwamna Dikko Ya Ƙaddamar da Aikin Faɗaɗa Titin Cikin Garin Mashi Mai Tsawon Kilomita Uku

Yadda Gwamna Raɗɗa ya ƙaddamar da aikin ginawa da faɗaɗa hanya a garin Mashi

14
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Gwamna Dikko Ya Ƙaddamar da Aikin Faɗaɗa Titin Cikin Garin Mashi Mai Tsawon Kilomita Uku

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Gwamnati Za Ta Samar Da Ingantaccen Tsarin Gudanar Da Makarantun Alƙu’rani A Jihar Katsina

Gwamnati Za Ta Samar Da Ingantaccen Tsarin Gudanar Da Makarantun Alƙu’rani A Jihar Katsina

August 13, 2026
An Samu Sauƙin Matsalar Tsaro: Yanzu Dukkan Kasuwanninmu Suna Ci

An Samu Sauƙin Matsalar Tsaro: Yanzu Dukkan Kasuwanninmu Suna Ci

August 12, 2026
Dikkon Katsinawa

__________
Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, PhD, CON ya ƙaddamar da aikin ginawa da faɗaɗa titin cikin garin Mashi mai tsawon kilomita uku, a wani mataki na ƙara inganta ababen more rayuwa da bunƙasa tattalin arzikin jihar.

Aikin, wanda zai gudana a kan babbar hanyar Katsina zuwa Daura, na daga cikin Shirin Sabunta Birane na gwamnatin jihar da ake aiwatarwa ƙarƙashin manufar “Building Your Future,” yayin da Kamfanin Mothercat Nigeria Limited zai gudanar da shi ƙarƙashin kulawar Ma’aikatar Ayyuka, Gidaje da Sufuri ta Jihar Katsina.

Da yake jawabi yayin ƙaddamar da aikin, Gwamna Radda ya bayyana cewa titin zai taimaka wajen inganta zirga-zirga, ƙara tsaron masu amfani da hanya, sauƙaƙa jigilar amfanin gona da sauran kayayyaki zuwa kasuwanni, rage kuɗaɗen sufuri, tare da ƙarfafa harkokin kasuwanci da tattalin arziki a Mashi da ma yankunan da ke kewaye da ita.

Ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da aiwatar da ayyukan da za su inganta rayuwar al’umma da kuma samar da ci gaba mai ɗorewa a sassa daban-daban na jihar.

Tun da farko, Kwamishinan Ayyuka, Gidaje da Sufuri na Jihar Katsina, Engr. Dr. Sani Magaji Ingawa, ya bayyana cewa aikin wani ɓangare ne na ƙudirin gwamnatin jihar na samar da ingantattun hanyoyi da suka dace da ƙa’idojin aikin zamani.

A cewarsa, aikin zai haɗa da gina magudanan ruwa na zamani, hanyoyin masu tafiya a ƙasa da kuma sanya fitilun kan titi masu amfani da hasken rana. Ya kuma tabbatar da cewa ma’aikatar za ta sanya ido sosai domin tabbatar da cewa an gudanar da aikin cikin inganci da bin ƙa’idojin da aka shimfiɗa.

Shi ma wakilin Kamfanin Mothercat Nigeria Limited ya gode wa Gwamnatin Jihar Katsina bisa amincewar da ta ba kamfanin, yana mai tabbatar da cewa za su gudanar da aikin bisa ƙa’idojin ƙwararru tare da kammala shi cikin wa’adin da aka tsara.

A madadin Mai Martaba Sarkin Katsina, Durɓin Katsina kuma Hakimin Mani, ya yaba wa Gwamna Raɗɗa bisa ci gaba da zuba jari a fannin ababen more rayuwa. Ya kuma isar da godiya da fatan alheri daga Mai Martaba Sarkin Katsina, tare da yin kira ga al’ummar yankin da su ba da cikakken haɗin kai domin tabbatar da nasarar aikin.
Shugaban Ƙaramar Hukumar Mashi ya bayyana cewa aikin zai taka muhimmiyar rawa wajen sauƙaƙa zirga-zirga da bunƙasa tattalin arzikin yankin.

Haka kuma, Shugaban Masu Ruwa da Tsaki na ƙaramar hukumar, Hon. Salisu Yusuf Majigiri, ya yaba wa Gwamna Raɗɗa bisa abin da ya bayyana a matsayin adalci da daidaito wajen rabon ayyukan ci gaba a faɗin jihar, tare da tabbatar masa da cikakken goyon bayan al’ummar Mashi.

A ƙarshen jawabinsa, Gwamna Radda ya umarci kamfanin da ke aiwatar da aikin da ya tabbatar da mafi girman inganci tare da kammala aikin cikin lokacin da aka tsara, yana mai jaddada cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da ba da fifiko ga ayyukan raya ƙasa da inganta jin daɗin al’ummar Jihar Katsina.

Bikin ƙaddamar da aikin ya samu halartar Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Katsina, Rt. Hon. Nasir Yahya Daura, mambobin Majalisar Zartarwa ta Jiha, ‘yan majalisa, sarakunan gargajiya, shugabannin ƙananan hukumomi, shugabannin siyasa da sauran al’umma.
__________

Previous Post

PEN WIZARD

Next Post

Governor Dikko Flags Off Construction, Expansion of 3-Kilometre Mashi Township Road

Related Posts

Gwamnati Za Ta Samar Da Ingantaccen Tsarin Gudanar Da Makarantun Alƙu’rani A Jihar Katsina
Labarai

Gwamnati Za Ta Samar Da Ingantaccen Tsarin Gudanar Da Makarantun Alƙu’rani A Jihar Katsina

August 13, 2026
An Samu Sauƙin Matsalar Tsaro: Yanzu Dukkan Kasuwanninmu Suna Ci
Labarai

An Samu Sauƙin Matsalar Tsaro: Yanzu Dukkan Kasuwanninmu Suna Ci

August 12, 2026
Katsina A Makon Jiya (Kashi Na Ɗaya)
Labarai

Katsina A Makon Jiya (Kashi Na Ɗaya)

August 10, 2026
Next Post
Governor Dikko Flags Off Construction, Expansion of 3-Kilometre Mashi Township Road

Governor Dikko Flags Off Construction, Expansion of 3-Kilometre Mashi Township Road

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Abin Da Ya Sa Na Naɗa Mataimaka 85 – Ciyaman Mukhtari City

Abin Da Ya Sa Na Naɗa Mataimaka 85 – Ciyaman Mukhtari City

September 18, 2025
ƘUNGIYAR HAUSAWA ZALLA: TA INA ZA A FARA KUMA DA WACE MANUFA? (5)

ƘUNGIYAR HAUSAWA ZALLA: TA INA ZA A FARA KUMA DA WACE MANUFA? (5)

May 24, 2025
Shugaba Tinubu Ya Sauke Shugabannin Rundunonin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Sauke Shugabannin Rundunonin Tsaro

June 19, 2023
Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (5)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (5)

February 11, 2026

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Tarihin Waƙar Yaƙin Tabuka

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Our Daily Message
  • Regulation, Standardisation of Qur’anic Schools Under Way in Katsina
  • Gwamnati Za Ta Samar Da Ingantaccen Tsarin Gudanar Da Makarantun Alƙu’rani A Jihar Katsina

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Our Daily Message

Our Daily Message

August 14, 2026
Regulation, Standardisation of Qur’anic Schools Under Way in Katsina

Regulation, Standardisation of Qur’anic Schools Under Way in Katsina

August 13, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.