• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Sunday, May 31, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Gizago

Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
April 16, 2026
in Gizago
0
Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

Malam Nasir El-rufa'i

38
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Rantsuwa Da Ƙur’ani: Martani Ga Shugaban Hausawan Bogi

Rantsuwa Da Ƙur’ani: Martani Ga Shugaban Hausawan Bogi

April 20, 2026
JOS! JOS!! JOS: Muhimmin Saƙo Zuwa Ga Musulmi Da Kirista

JOS! JOS!! JOS: Muhimmin Saƙo Zuwa Ga Musulmi Da Kirista

April 3, 2026
Malam Nasir El-rufa’i

 

__________

Malam Nasir El-rufa’i, mutumin da sunansa ya buga tambari a zukatan mutane a ƙasar nan. Rayuwarsa cike take da ƙalubale. Tun daga lokacin da sunansa ya bayyana a Gwamnatin Obasanjo a 2000 zuwa yau da muke ciki, 2026, bai taɓa ɓuya ba. A wannan nazari, za mu bibiyi irin waɗannan ƙalubale da ya fuskanta.

Malam Nasir, tsohon Gwamnan Jihar Kaduna ne wanda ya shahara wajen aiwatar da manufofi masu tsauri da kuma sauye-sauye a harkokin gwamnati. An haife shi a 1960 kuma ya fara fitowa fili a siyasar ƙasar nan a farkon shekarun 2000. Rayuwarsa ta ƙunshi hawa da sauka da suka danganci muƙaman gwamnati zuwa lokutan ƙalubale da rikice-rikice da kuma nasara.

A zamanin mulkin Olusegun Obasanjo (1999–2007), El-Rufa’i ya fara aiki a matsayin Darakta Janar na Hukumar Kula Da Kadarorin Ƙasa (Bureau of Public Enterprises) daga 2003 zuwa 2007, inda ya jagoranci shirye-shiryen sayar da kamfanonin gwamnati. Daga bisani, ya zama Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT) daga 2003 zuwa 2007. A wannan lokaci, ya gudanar da rusau da gyaran Abuja domin bin tsarin birnin, wanda ya jawo masa suka da ƙalubale daga jama’a da ‘yan siyasa daban-daban.

A wannan lokaci (2003–2007), ya fuskanci manyan matsaloli, ciki har da adawa daga masu ruwa da tsaki da kuma zarge-zargen rashin tausayi ga talakawa. Duk da haka, ya samu goyon baya daga Gwamnatin Obasanjo saboda jajircewarsa wajen aiwatar da manufofi ba tare da tsoro ba.

Bayan saukar Obasanjo daga mulki a 2007, a zamanin Umaru Musa Yar’Adua (2007–2010), rayuwar El-Rufai ta sauya. A daidai lokacin ya bar Najeriya, ya koma ƙasashen waje, musamman Amurka da wasu ƙasashe, sakamakon matsin lamba na siyasa da bincike da ake zargin ana yi masa. Wannan lokaci ya kasance kamar na gudun hijira a gare shi.

Daga 2010 zuwa 2014, bayan rasuwar Yar’adua da dawowar sauyin siyasa, El-Rufai ya fara dawowa Najeriya a hankali. A wannan lokaci, ya shiga harkokin siyasa a jam’iyyar CPC, sannan daga baya jam’iyyar ta shiga haɗaka, ta rikiɗe zuwa APC.

A shekarar 2015, El-Rufai ya zama Gwamnan Jihar Kaduna, inda ya yi mulki daga 2015 zuwa 2023 a ƙarƙashin jam’iyyar APC. A wa’adinsa na farko (2015–2019), ya mayar da hankali kan gyaran ilimi, rage kashe kuɗin gwamnati da kuma sake fasalin ma’aikata. Amma ya fuskanci ƙalubale, musamman kamar rikicin Kudancin Kaduna, matsalar ‘yan Shi’a mabiya Sheikh Eizakzaky da matsalolin tsaro da sauransu.

A wa’adinsa na biyu (2019–2023), ya ci gaba da manufofinsa masu tsauri, ciki har da sallamar ma’aikata da sake tsarin makarantu. Kodayake ya samu wasu nasarori, musamman wajen samar da gine-gine amma ya fuskanci suka daga ƙungiyoyin ƙwadago da jama’a da kuma matsalolin tsaro da suka ci gaba da addabar al’ummar jihar.

Bayan kammala mulkinsa a 2023, ya taka muhimmiyar rawa wajen kafa Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu, inda a farko aka bayyana shi a matsayin wanda za a naɗa Minista amma daga bisani Majalisar Dattawa ta hana tabbatar da naɗin nasa. Wannan ya zama babban ƙalubale a rayuwarsa ta siyasa, domin kuwa shi ne dalilin da ya sanya ya raba gari da Gwamnatin Tinubu. Daga bisani ma ya fita daga Jam’iyyar APC zuwa SDP, sannan kuma zuwa ADC.

Daga 2023 zuwa yanzu (2026), El-Rufai na fuskantar ƙalubalen da suka haɗa da na batutuwan shari’a tsakaninsa da Gwamnatin Tinubu da ta Uba Sani a Jihar Kaduna. A kan haka ake ta jerangiya da shi, daga Hukumomin ICPC da EFCC, inda yake tsare sama da wata ɗaya, kodayake a zaman shari’ar da aka yi a wannan makon, an amince da belinsa bisa tsausaran sharuɗɗan da idan ya cika su za a sake shi kuma a ci gaba da fafata shari’a.

Malam Nasiru ya zama gugar ƙarfe, sha kwaramniya. Ko yaya makomarsa za ta kasance a nan gaba? Ko akwai yiwuwar zai sake zama mai tasiri bayan kammala wannan shari’a, ko kuwa hasken siyasarsa zai dusashe? Shin ko zai iya dawowa da ƙarfi kamar yadda ya taɓa yi a baya? Allah ne kaɗai masani!

__________

Previous Post

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

Next Post

Mu Ji Tsoron Allah

Related Posts

Rantsuwa Da Ƙur’ani: Martani Ga Shugaban Hausawan Bogi
Gizago

Rantsuwa Da Ƙur’ani: Martani Ga Shugaban Hausawan Bogi

April 20, 2026
JOS! JOS!! JOS: Muhimmin Saƙo Zuwa Ga Musulmi Da Kirista
Gizago

JOS! JOS!! JOS: Muhimmin Saƙo Zuwa Ga Musulmi Da Kirista

April 3, 2026
Najeriya 2027: Matsalolin Da Za Su Iya Wargaza Takarar Obi Da Kwankwaso
Gizago

Najeriya 2027: Matsalolin Da Za Su Iya Wargaza Takarar Obi Da Kwankwaso

March 29, 2026
Next Post
Mu Ji Tsoron Allah

Mu Ji Tsoron Allah

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

An Kafa Gidauniyar Danbarno

An Kafa Gidauniyar Danbarno

June 30, 2023
SAƘON JUMU’A: Daga Malam Anas Saminu Ja’en

SAƘON JUMU’A: Daga Malam Anas Saminu Ja’en

October 6, 2023
Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawa Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (4)

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawa Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (4)

January 2, 2026
GODIYA

GODIYA

March 3, 2024

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • POSITIVE COMRADE
  • BUKAR USMAN: The Human Library
  • Sule Lamido’s Theme of Authenticity

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

POSITIVE COMRADE

POSITIVE COMRADE

May 20, 2026
BUKAR USMAN: The Human Library

BUKAR USMAN: The Human Library

May 19, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.