• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Monday, April 6, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Babban Labari

Yadda Babban Jigon Jam’iyyar APC Daga Kano Ya Mutu A Otel

BABBAN LABARI

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
April 2, 2026
in Babban Labari
0
Yadda Babban Jigon Jam’iyyar APC Daga Kano Ya Mutu A Otel

Marigayi Alhaji Abdulsalam Ginsau

100
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Yadda Babban Jigon Jam’iyyar APC Daga Kano Ya Mutu A Otel

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Gwamnan Jigawa Ya Amso Walida Daga Hukumar DSS

Gwamnan Jigawa Ya Amso Walida Daga Hukumar DSS

February 26, 2026
Wata Mata Ta Haifi “Hatsabiban Jarirai” A Ofishin Hukumar NDLEA

Wata Mata Ta Haifi “Hatsabiban Jarirai” A Ofishin Hukumar NDLEA

February 22, 2026
Marigayi Alhaji Abdulsalam Ginsau

 

__________

An samu cikakken rahoton da ke tabbatar da yadda Mataimakin Sakataren Tsare-Tsare na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano, Abdulsalami Ginsau ya rasu a otel ɗin Chida Hotels da ke yankin Utako a Abuja.

Ginsau, wanda lauya ne, shi ne shugaban kwamitin da aka ɗora wa alhakin shirya masaukai ga wakilan Jihar Kano da suka halarci babban taron APC da aka kammala kwanan nan a Abuja.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa ya rasu ne a ranar Juma’a, 27 ga Maris, bayan da ake zargin ya maƙale a cikin lalatattar lifta (elevator) a cikin otel ɗin.

Da yake magana kan lamarin, Shugaban Jam’iyyar APC na Jihar Kano, Umar Haruna Doguwa ya ce Ginsau, a matsayinsa na wanda aka ɗora wa alhakin samar da masaukai ga wakilai, ya isa Abuja tun kwana guda kafin taron, domin ya kama ɗakuna ga mahalarta taron daga jihar.

Ya ce bayan ya kammala shirya wa wakilan masaukai, Ginsau ya sauka a otel ɗin Chida Hotels. Doguwa ya ce sun fara zargin akwai matsala, lokacin da ba su ga Ginsau ba a yayin taron a ranar Juma’a, wanda ya sa suka fara nemansa, domin sanin inda ya maƙale.

Ya ce a yayin binciken da suka yi a ko’ina cikin Abuja, sun je ofishin ‘yan sanda na Utako domin kai rahoto, inda aka sanar da su cewa an samu wani lamari a otel ɗin Chida, wanda aka kawo masu rahoto.

Doguwa ya ce da suka isa otel ɗin, sun gano gawar marigayi Ginsau, inda ya ɗora laifin rasuwarsa ga sakacin hukumar gudanarwa ta otel ɗin.

A cewarsa, wasu wakilai da ke zaune a otel ɗin, sun taɓa nuna damuwa, cewa liftar otel ɗin tana da matsala. Ya ce an kai gawar mamacin domin a yi binciken sanadin mutuwarsa kuma suna jiran sakamakon binciken ‘yan sanda.

Wata majiyar ‘yan sanda ta bayyana cewa, mahukuntan Chida Hotels sun kai rahoton lamarin a hedikwatar ofishinsu a ranar Asabar, 28 ga Maris, kuma ana ci gaba da bincike.

“Chida Hotels sun zo sun bayar da rahoton cewa an samu wani lamari kuma muna bincikensa. Nazarin gawar da ake yi wani ɓangare ne na binciken. Ofishin yana ci gaba da bincike sosai,” in ji majiyar.

Lokacin da aka tuntuɓi manajan otel din, Princess Oluchi, ta ce ba za su yi wani bayani ba saboda ana ci gaba da binciken ‘yan sanda. Sai dai wata majiya a cikin otel ɗin ta yi ƙarin bayani kan abin da ya faru.

Dangane da abin da ya faru, wata majiya daga otel ɗin ta ce ɗaya daga cikin liftocin otel ɗin ta lalace kuma aka tilasta buɗe ta. Ta ƙara da cewa marigayin wanda ke zaune a hawa na uku, ya fito daga ɗakinsa ya shiga lifta ɗin da ta lalace da sassafe ranar Juma’a, inda a cikin wannan yanayi liftar ta nutse da shi a ciki ba tare da mahukuntan otel ɗin sun sani ba.

A wannan lokaci, duk wakilan da ke zaune a otel ɗin sun tafi wajen taron, ba tare da sanin cewa wani mummunan abu ya faru ba.

Majiyar ta ce washegari ne otel ɗin ya fara jin wari mai muni, wanda ya sa aka fara bincike, inda aka gano gawar marigayin.

Da yake magana a madadin iyalan, wani mai kula da marigayin, Hamza Haladu, ya bayyana lamarin a matsayin abin mamaki, yana mai cewa marigayin yana cikin ƙoshin lafiya kafin tafiyarsa Abuja.

“Yana cikin ƙoshin lafiya kuma cike da kuzari lokacin da ya tafi. Labarin rasuwarsa ya zo mana a matsayin babban abin mamaki,” in ji shi.

Marigayi Ginsau, fitaccen lauya kuma jigo a jam’iyya, an zaɓe shi kwanan nan a matsayin Sakataren Tsare-Tsare na Jam’iyyar APC a Jihar Kano.

Ya taɓa zama Babban Daraktan Kamfanin Ginsau & Sons kuma ya yi aikin lauya a Ginsau & Co. Advocates. An san shi da ƙwarewa a fannin dokokin kamfanoni da kasuwanci. Haka kuma ya riƙe muƙamin lauya a H.H. Karkasara & Co., inda ya ƙware a fannin kadarori, haraji da sauransu.

Ya yi karatu a Jami’ar Musulunci da ke Uganda da kuma Makarantar Lauyoyi ta Najeriya da ke Abuja, inda ya gina sana’ar da ta haɗa shugabanci a kasuwanci da kuma aikin lauya.

A cikin APC, ana kallonsa a matsayin jigo, wanda tasirinsa ya wuce harkokin Shari’a, domin yana da ƙwarewa a fannin dabarun siyasa da shugabanci. Ya rasu ya bar mata biyu da ‘ya’ya biyu.

__________

Previous Post

Plateau Massacre/American National: Open Letter to the NSA Malam Nuhu Ribadu

Next Post

JOS! JOS!! JOS: Muhimmin Saƙo Zuwa Ga Musulmi Da Kirista

Related Posts

Gwamnan Jigawa Ya Amso Walida Daga Hukumar DSS
Babban Labari

Gwamnan Jigawa Ya Amso Walida Daga Hukumar DSS

February 26, 2026
Wata Mata Ta Haifi “Hatsabiban Jarirai” A Ofishin Hukumar NDLEA
Babban Labari

Wata Mata Ta Haifi “Hatsabiban Jarirai” A Ofishin Hukumar NDLEA

February 22, 2026
Musulmin Kudancin Najeriya Sun Jaddada Mubaya’a Ga Sarkin Musulmi
Babban Labari

Musulmin Kudancin Najeriya Sun Jaddada Mubaya’a Ga Sarkin Musulmi

February 13, 2026
Next Post
JOS! JOS!! JOS: Muhimmin Saƙo Zuwa Ga Musulmi Da Kirista

JOS! JOS!! JOS: Muhimmin Saƙo Zuwa Ga Musulmi Da Kirista

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

 KADARKO

 KADARKO

February 8, 2024
Huɗubar Jumu’a A Taƙaice Daga Masallacin Tumbu-Madalla

Huɗubar Jumu’a A Taƙaice Daga Masallacin Tumbu-Madalla

July 21, 2023
Hafsat Nasir Umar: ‘Yar Jaridar Da Ba Ta San Kasala Ba

Hafsat Nasir Umar: ‘Yar Jaridar Da Ba Ta San Kasala Ba

July 2, 2023
ABIN DA YA SA AKE RAINA MAGANAR WASU “MALAMAI”

ABIN DA YA SA AKE RAINA MAGANAR WASU “MALAMAI”

July 16, 2024

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Double or Die: Thrills, Suspense and Puzzles
  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (9)
  • JOS! JOS!! JOS: Muhimmin Saƙo Zuwa Ga Musulmi Da Kirista

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Double or Die: Thrills, Suspense and Puzzles

Double or Die: Thrills, Suspense and Puzzles

April 5, 2026
Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (9)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (9)

April 4, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.