Yunƙurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (14)
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

__________
√ Wani Salon Makirci Daga Hausawan Bogi
Yana daga cikin makirci da munafunci da alayen haddasa fitina na masu iƙirarin Hausa Zalla, yadda za ka ji suna yin kuɗin goro ga al’ummar Fulani, suna kiran su da ‘yan ta’adda.
A kullum za ka ji suna kiran shugabannin ƙungiyoyin Fulani da cewa wai su sanya baki, domin Fulanin Daji su daina ta’addanci amma kuma ba su yin kira ga gwamnati da ta ɗauki matakin da ya dace a kan DUK ‘YAN TA’ADDA da suka addabi al’umma a kowane sashi na ƙasar nan.
Abin tambaya shi ne, shin sun manta da cewa shi ɗan ta’adda babu ruwansa da ƙabila, addini ko sashin da mutum ya fito? Shin sun manta da cewa Shugabannin Fulani su ma gama-garin mutane ne da ba su da makami ko ikon hukunci a hannunsu?
Idan dai gaskiya ake so, to GWAMNATI ita ce mai iko. Ita take da makaman yaƙi, ita take da sojoji da ‘yan sanda da DSS da sauran jami’an tsaro.
Me zai hana gaba ɗaya mu nemi ita gwamnatin ta yi abin da ya dace?
Me zai hana gwamnatin ta yi bincike ta zaƙulo duk wani ɗan ta’adda da ke ƙasar nan, da mai ɗaure masa gindi, da mai samar masa da makami (kowane ne) ta kama shi, ta hukunta shi?
Mu dai har kullum ba za mu gushe ba, za mu ci gaba da faɗin gaskiya, cewa ta’addanci a ƙasar nan ba kayan wata ƙabila ɗaya ba ne. Aiki ne na bijirarrun mutanen da suka sanya kansu cutar da al’umma. A kowace ƙabila, akwai ‘yan ta’adda.
Don haka a daina yin kuɗin goro. WANDA DUK YA YI LAIFI, ko shi ɗan wace ƙabila ne, ko shi wane addini yake bi, ko daga wace shiyya yake, AIKIN GWAMNATI ne ta kama shi ta hukunta shi, daidai da laifinsa. Wannan shi ne adalci kuma shi zai kawo zaman lafiya da kwanciyar hankali a ƙasa.
Lallai ne mu sani, rashin hukunta masu laifi, shi ya sanya ta’addanci ya ta’azzara! Amma muddin gwamnati ta yi abin da ya dace, to babu shakka za a samu lafiya!
___________













